Ilimi
Gwamna Namadi Tare Da Hadin Gwiwar Kasar Qatar Sun Samar Da Cibiyar Bunkasa Ilimi A Jigawa
Gwamna Mallam Umar Namadi ya kaddamar da Cibiyar Al’amuran Addinin Musulunci a kauyen Babbar Riga dake karamar hukumar Malam-Madori a jihar Jigawa.
Cibiyar wacce aka ginata tare da hadin gwiwar wata kungiyar Agaji ta kasar Qatar mai zaman kanta da kuma gwamnatin jihar Jigawa, an tsara shi ta ne domin kawo sauyi ga al’umma ta kyautata rayuwarsu, da samar da ingantaccen ilimi.

Sabuwar cibiyar da aka kaddamar ta kunshi rukunin gidaje, da ginin makaranta na zamani, da masallaci, wadanda za su samar da yanayi mai kyau na koyo da ci gaban al’umma.
Wannan shiri ya jaddada kudirin gwamnatin jihar Jigawa na bunkasa ilimi da inganta rayuwar al’umma.

A yayin bikin, Gwamna Namadi ya yabawa kungiyar Qatar Charity bisa sadaukarwar da ta yi, sannan ya bukaci a ci gaba da hada kai don fadada irin wadannan ayyuka a fadin jihar Jigawa.
Ya sanar da cewa hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar (SUBEB) za ta kula da wurin domin tabbatar da kulawar da ta dace, tare da samar da malamai da sauran kayayyakin aiki a makarantar.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Jigawa, Hamisu Mohammed Gumel ya fitar, ya ce bikin kaddamarwar ya samu halartar manyan baki da suka hada da jakadan Qatar a Najeriya, Ali Bin Ghanem Al-Hajri; da Daraktan kungiyar agaji ta Qatar, Hamdi Abdou.

Sauran sun hada da Darakta-Janar na Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Kasa (NITDA), Kashifu Abdullahi; da Sarkin Hadejia, Alhaji Adamu Abubakar Maje; da sauran fitattun shugabanni da sauran al’umma.
Kungiyar Qatar Charity ta mikawa gwamnatin jihar Jigawa ginin a hukumance, inda al’ummar yankin suka fara amfani da ita.

Mista Hamdi Abdou, daraktan kungiyar agaji na kasar, ya yabawa Gwamna Namadi bisa hangen nesa, tare da yin alkawarin ci gaba da kawo dauki a jihar Jigawa a wannan shekarar ta 2025.
Wannan aiki na nuni da cika alkawarin da Qatar Charity ta yi a lokacin da Gwamna Namadi ya ziyarci ofishinsu na Abuja a shekarar da ta gabata.

Da wannan hadin gwiwa, jihar Jigawa na ci gaba da kafa tarihi na hadin gwiwa mai ma’ana da nufin magance kalubalen ilimi da gidaje, da samar da ci gaba mai dorewa ga al’ummarta.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
