Labarai
Guguwa ta kashe mutum daya, ta kuma lalata gidaje sama da 100 a Nasarawa

Wata kakkarfar Guguwar ta kashe mutum daya tare da jikkata wasu da dama tare da lalata gidaje sama da dari a Agbashi da ke karamar hukumar Doma a jihar Nasarawa.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, mataimakin shugaban karamar hukumar Doma Mista John Bako – Ari, ya ce abin takaicin ya faru ne a ranar Talata da yamma.
A cewarsa, sama da gidaje dari ne aka lalata da suka hada da babban masallacin Agbashi, wani bangare na makarantar furamare ta Agbashi da sauran kayayyakin more rayuwa da dama na jama’a.
“A gaskiya guguwar ta lalata gidaje sama da 100 da suka hada da, masallaci da kuma makarantar Firamare, lamarin ya faru ne jiya da yamma,” inji shi.
Shima da yake magana akan lamarin, mukaddashin shugaban kungiyar ci gaban Agbashi, Mista Anthony Oshinyeka, mukaddashin shugaban kungiyar ci gaban yankin, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.
Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta gaggauta kawo dauki domin dakile mummunar barnar da al’ummar Agbashi ke fama da shi.
Mukaddashin Shugaban kungiyar ya nemi da a gaggauta bada kayan agaji daga gwamnati da masu hannu da shuni ga al’ummomin da abin ya shafa.
Aliyu Muraki/Lafia/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
