Labarai
Gobara Ta Babbake Wani Gida Mai Dakuna Hudu A Jihar Kwara
Wata gobara da ta taso dalilin wutar lantarki ta lalata wani katafaren gida mai dakuna hudu a unguwar Orisunbare da ke unguwar Amoyo a jihar Kwara.
A cikin wata sanarwa da shugaban hukumar kashe gobara ta jihar Kwara Hassan Adekunle ya fitar, ya ce hukumar kashe gobara ta jihar ta samu kiran da aka yi ta samun rahoton barkewar gobara a gida mai lamba 35 a yankin Orisunbare.
A cewarsa da isar su, ma’aikatan kashe gobarar sun sami wani gida yana cin wuta gangaa ba tare da bata lokaci ba jami’ai suka shiga aikin sui, inda suka nuna kwarewa, jajircewa, da kuma kwarewa.
Sanarwar ta bayyana cewa, saboda jinkirin bayar da rahoto, gidan ya riga ya sami matsala sosai kafin isowar su.
Sanarwar ta ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa gobarar ta tashi ne sakamakon wani karin wuta da aka yi, inda ta kara da cewa kasancewar kayan dake cin wuta cikin sauri na da dama a cikin gidan ya taimaka wajen kara ruruwar wutar.
Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kwara, Prince Falade John, ya jaddada mahimmancin bin matakan kiyaye kashe gobara domin kaucewa faruwar haka nan gaba.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
