Ilimi
Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya reshen jihar Kano, ta bayyana cewa Fursunoni 58 suna rubuta Jarrabawar Kammala Sakandare ta Kasa NECO ta shekarar 2025.
Wannan ci gaba ya samu ne bayan biyan kudin rajista da gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Musbahu Kofar-Nasarawa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Kano.
Ya ce wannan karamci na gwamnatin jihar Kano shaida ce ta jajircewarta wajen kula da walwalar fursunoni, gyaran dabi’unsu da kuma dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata.
“Biyan kudin rajistar jarrabawa da gwamnatin Kano ta yi alama ce ta jajircewarta wajen samar da dama ga fursunoni domin su gyara rayuwarsu su koma cikin al’umma,” in ji shi.
Hukumar ta bayyana godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa goyon bayansa da hadin kai da yake bayarwa ba kakkautawa.
Ya ce wannan mataki zai karfafa gwiwar fursunoni wajen daukar karatu da muhimmanci tare da ba su wata sabuwar dama ta samun ilimi da kyakkyawar makoma.
Musbahu Kofar-Nasarawa ya kara da cewa, hukumar gyaran hali ta Kano ta kuduri aniyar samar da kyakkyawan yanayi domin gyaran hali da ilimantar da fursunoni.
“Muna alfahari da samun goyon bayan gwamnatin Kano a wannan kokari,” in ji sanarwar.
Ya kuma ce jajircewar hukumar wajen gyaran hali na bayyana ta hanyoyin da take bi wajen samar wa da fursunoni damar samun ilimi da sauran damammaki da za su taimaka musu su gyara rayuwarsu su koma cikin al’umma.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
