Connect with us

Ilimi

Farfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya ta Dutse (FUD), Farfesa Ahmad Mohammed Gumel, ya bayyana cikakken shiri da zai sauya jami’ar zuwa cibiyar bincike, kirkire-kirkire da kuma ingantaccen ilimi a Najeriya nan da shekarar 2030.

Farfesa Ahmad Gumel ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da manufofinsa lokacin da ya karɓi ragamar aiki a hukumance a matsayin Shugaban jami’ar na huɗu.

Ya jaddada muhimmancin samar da ɗaliban da ke da ƙwarewa, nagarta da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.

A cewarsa, wannan shirin sauyi yana tafiya ne bisa wani tsarin bunƙasa jami’a mai manufofin goma sha ɗaya, inda aka fi bai wa fannonin inganta ilimi, bincike da kirkire-kirkire, bunƙasa fasahar zamani, da inganta jin daɗin ɗalibai da ma’aikata muhimmanci.

Ya bayyana cewa jami’ar za ta sabunta tsarin karatunta domin ya dace da ƙa’idojin Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da kuma kyawawan ƙa’idojin ilimi na duniya, tare da shirin ƙaddamar da sabbin shirye-shiryen karatu kamar Fasahar Basirar Na’ura (Artificial Intelligence), Kimiyyar Bayanai (Data Science), Cloud Computing, Noman da ya dace da sauyin yanayi (Climate-Smart Agriculture), da sauran sabbin fannoni.

Shugaban jami’ar ta FUD ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa an tsara cikakken shirin bunƙasa jami’ar na shekaru biyar, wanda nan ba da jimawa ba za a gabatar da shi ga majalisar gudanarwa domin amincewa.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara