Ilimi
Farfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
Daga Usman Muhammad Zaria
Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya ta Dutse (FUD), Farfesa Ahmad Mohammed Gumel, ya bayyana cikakken shiri da zai sauya jami’ar zuwa cibiyar bincike, kirkire-kirkire da kuma ingantaccen ilimi a Najeriya nan da shekarar 2030.
Farfesa Ahmad Gumel ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da manufofinsa lokacin da ya karɓi ragamar aiki a hukumance a matsayin Shugaban jami’ar na huɗu.

Ya jaddada muhimmancin samar da ɗaliban da ke da ƙwarewa, nagarta da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.
A cewarsa, wannan shirin sauyi yana tafiya ne bisa wani tsarin bunƙasa jami’a mai manufofin goma sha ɗaya, inda aka fi bai wa fannonin inganta ilimi, bincike da kirkire-kirkire, bunƙasa fasahar zamani, da inganta jin daɗin ɗalibai da ma’aikata muhimmanci.


Ya bayyana cewa jami’ar za ta sabunta tsarin karatunta domin ya dace da ƙa’idojin Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da kuma kyawawan ƙa’idojin ilimi na duniya, tare da shirin ƙaddamar da sabbin shirye-shiryen karatu kamar Fasahar Basirar Na’ura (Artificial Intelligence), Kimiyyar Bayanai (Data Science), Cloud Computing, Noman da ya dace da sauyin yanayi (Climate-Smart Agriculture), da sauran sabbin fannoni.

Shugaban jami’ar ta FUD ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa an tsara cikakken shirin bunƙasa jami’ar na shekaru biyar, wanda nan ba da jimawa ba za a gabatar da shi ga majalisar gudanarwa domin amincewa.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
