Connect with us

Kasuwanci

Coci-coci a Kurmin Walin Jihar Kaduna Sun Gudanar da Ibada Bayan Garkuwa da Mutane

Published

on

An gudanar da ibadar Lahadi a ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro a al’ummar Kurmin Wali da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna, biyo bayan garkuwa da mazauna 166 da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi a makon da ya gabata.

Ziyarar da Rediyo Nijeriya ta kai yankin ta nuna cewa yawan masu halartar ibada ya ragu ƙwarai a coci-coci uku da lamarin ya shafa, sakamakon yadda da dama daga cikin masu ibada ke cikin waɗanda aka sace, yayin da wasu kuma suka tsere daga yankin saboda fargabar sake kai hari. Yanayin ibadar ya kasance cike da jimami, inda aka fi mayar da hankali wajen yin addu’o’in dawo da waɗanda aka sace lafiya da kuma kawo zaman lafiya a yankin da ke fama da matsalar tsaro.

Da yake zantawa da wakilinmu, Sakataren Cocin Cherubim and Seraphim Church Two, Mista Jonathan Na’allah, ya ce babban abin da ke damun mambobin cocin shi ne lafiya da tsaron ‘yan uwansu da ke hannun masu garkuwa. Ya kara da cewa mazauna yankin na ci gaba da rayuwa cikin fargaba da tashin hankali sakamakon yawan faruwar sace-sace a al’ummar. Sai dai ya ce ganin jami’an tsaro a fili yayin ibadar ya dan ba masu ibada kwanciyar hankali.

An kuma gudanar da ibada ta haɗin gwiwa tsakanin Cocin ECWA da Cherubim and Seraphim Church One a wuri guda, inda mambobi suka yi addu’o’in neman taimakon Ubangiji da kuma nasarar kokarin gwamnati na shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

Shugabannin coci-cocin, Malam Danjuma Wali da Mista Yunana Adauji, sun yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna bisa alkawarin inganta ababen more rayuwa a yankin. Sai dai sun yi kira da a dauki mataki cikin gaggawa domin ganin an saki waɗanda aka sace, suna mai jaddada cewa al’ummar ba za ta koma rayuwa ta yau da kullum ba matuƙar har yanzu da dama na hannun ‘yan bindiga.

A halin yanzu, Gwamnatin Jihar Kaduna ta fara daukar matakai domin cika alkawuran da ta dauka na ababen more rayuwa, inda aka tura manyan motoci da injinan aiki zuwa hanyar da ke shiga al’ummar domin fara ayyukan ginata. Wannan ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Uba Sani ya yi yayin ziyararsa Kurmin Wali jim kaɗan bayan faruwar lamarin garkuwa da mutane.

Mazauna yankin sun bayyana fatan alheri cewa dorewar aikin tsaro da kuma ayyukan ci gaba da aka yi alkawari za su taimaka wajen maido da kwarin gwiwa da zaman lafiya a al’ummar.

COV / Shindong Bala

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara