Kasuwanci
Coci-coci a Kurmin Walin Jihar Kaduna Sun Gudanar da Ibada Bayan Garkuwa da Mutane
An gudanar da ibadar Lahadi a ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro a al’ummar Kurmin Wali da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna, biyo bayan garkuwa da mazauna 166 da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi a makon da ya gabata.
Ziyarar da Rediyo Nijeriya ta kai yankin ta nuna cewa yawan masu halartar ibada ya ragu ƙwarai a coci-coci uku da lamarin ya shafa, sakamakon yadda da dama daga cikin masu ibada ke cikin waɗanda aka sace, yayin da wasu kuma suka tsere daga yankin saboda fargabar sake kai hari. Yanayin ibadar ya kasance cike da jimami, inda aka fi mayar da hankali wajen yin addu’o’in dawo da waɗanda aka sace lafiya da kuma kawo zaman lafiya a yankin da ke fama da matsalar tsaro.
Da yake zantawa da wakilinmu, Sakataren Cocin Cherubim and Seraphim Church Two, Mista Jonathan Na’allah, ya ce babban abin da ke damun mambobin cocin shi ne lafiya da tsaron ‘yan uwansu da ke hannun masu garkuwa. Ya kara da cewa mazauna yankin na ci gaba da rayuwa cikin fargaba da tashin hankali sakamakon yawan faruwar sace-sace a al’ummar. Sai dai ya ce ganin jami’an tsaro a fili yayin ibadar ya dan ba masu ibada kwanciyar hankali.
An kuma gudanar da ibada ta haɗin gwiwa tsakanin Cocin ECWA da Cherubim and Seraphim Church One a wuri guda, inda mambobi suka yi addu’o’in neman taimakon Ubangiji da kuma nasarar kokarin gwamnati na shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar yankin.
Shugabannin coci-cocin, Malam Danjuma Wali da Mista Yunana Adauji, sun yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna bisa alkawarin inganta ababen more rayuwa a yankin. Sai dai sun yi kira da a dauki mataki cikin gaggawa domin ganin an saki waɗanda aka sace, suna mai jaddada cewa al’ummar ba za ta koma rayuwa ta yau da kullum ba matuƙar har yanzu da dama na hannun ‘yan bindiga.
A halin yanzu, Gwamnatin Jihar Kaduna ta fara daukar matakai domin cika alkawuran da ta dauka na ababen more rayuwa, inda aka tura manyan motoci da injinan aiki zuwa hanyar da ke shiga al’ummar domin fara ayyukan ginata. Wannan ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Uba Sani ya yi yayin ziyararsa Kurmin Wali jim kaɗan bayan faruwar lamarin garkuwa da mutane.
Mazauna yankin sun bayyana fatan alheri cewa dorewar aikin tsaro da kuma ayyukan ci gaba da aka yi alkawari za su taimaka wajen maido da kwarin gwiwa da zaman lafiya a al’ummar.
COV / Shindong Bala
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
