Connect with us

Labarai

Cikar Jigawa Shekaru 34: Gwamna Namadi Ya Yabawa Tsoffin Shugabanni

Published

on

Gwamna Malam Umar Namadi ya yaba wa shugabannin da suka gabata bisa jajircewa da sadaukarwar da suka yi wajen shimfiɗa tubalin ci gaban jihar tun daga shekarar 1991 zuwa yau.

A taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, gwamnan ya ce bikin cika shekaru 34 da kafuwar jihar dama ce ta tunawa, tare da murna da kuma sabunta aniyar ci gaban Jigawa.

Ya bayyana cewa jihar ta samu sauyi a fannoni da dama ciki har da noma, ilimi, kiwon lafiya, hanyoyi da ci gaban zamantakewa. A cewarsa, gwamnatinsa za ta ci gaba da kokari kan waɗannan nasarori tare da bullo da sabbin hanyoyi na bunƙasa jihar.

Namadi ya jaddada kudurinsa na aiwatar da manufofin gwamnatinsa 12, wadanda suka haɗa da samar da ayyukan yi, haɓaka noma, inganta kiwon lafiya da ilimi, da kuma raya ababen more rayuwa.

Ya ce gwamnati ta kaddamar da manyan shirye-shirye a fannoni da dama ciki har da injinan noma, ilimi, kiwon lafiya, hanyoyi da kuma tallafa wa matasa, domin inganta hidima da tabbatar da kyakkyawan shugabanci.

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su haɗa hannu wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban jihar, yana mai cewa “Ci gaban Jigawa alhaki ne na kowa.”

Ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da inganta tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da jinƙai, domin rage talauci da inganta rayuwar jama’a.

A ƙarshe, Gwamna Namadi ya gode wa jama’ar Jigawa bisa goyon bayan da suke ba shi, yana mai alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta kasance mai gaskiya da rikon amana akoda yaushe.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara