Connect with us

Labarai

Arewa Cohesion Ta Kaddamar da Shuwagabani Na Jihohi Da Kwamitoci Don Inganta Hadin Kai Da Cigaba

Published

on

 

Kungiyar Arewa Cohesion for Peace, Unity and Development Initiative ta kaddamar da shuwagabanin jihohi da kwamitoci na dindindin domin ƙarfafa tushen aikin kungiyar.

 

Daraktan Gidauniyar, Dr. Abdullahi Idris, ne ya bayyana haka a wajen bikin kaddamarwar da aka gudanar a Arewa House, Kaduna.

 

Kwamitocin da aka kaddamar sun haɗa da: kwamitin tsare-tsare da dabaru, kwamitin kudi da kwamitin kula da Jama’a, tare da shuwagabanin jihohi na rikon kwarya na kungiyar.

 

Dr. Abdullahi Idris ya bayyana cewa waɗannan sabon tsarin zai taimaka wajen ganin kungiyar ta zauna yanda ya kamata da hangen nesa da zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba mai ɗaurewa a Arewacin Najeriya.

 

Ya kuma yi bayanin ayyukansu kamar haka, Kwamitin Tsare-tsare da Dabaru zai kula da tsara manufofi, fifita manyan ayyuka, da gano abokan hulɗa don tabbatar da cimma manufofin kungiyar.

 

A kan Kwamitin Kudi kuwa, ya jaddada muhimmancin tara kudade, yin amfani da su cikin hikima, tare da kiyaye gaskiya da lissafi na nagarta.

 

Dr. Abdullahi Idris ya tabbatar da cewa dorewar kudi da kyakkyawan gudanarwa ne za su tabbatar da nasarar kungiyar nan gaba.

 

Haka kuma ya jaddada muhimmancin Kwamitin Hula da Jama’a, inda ya bayyana shi a matsayin murya da hoto na kungiyar.

 

A cewarsa, kwamitin zai inganta sunan kungiyar a idon jama’a, ya yaƙi labaran ƙarya, ya kuma tabbatar da ingantacciyar kafuwa a kafofin yada labarai na gargajiya da na zamani, domin Arewa Cohesion ta zama suna sananne a cikin gida da wajen gida.

 

Game da matakin ƙasa kuwa, Daraktan ya haskaka rawar da Kwamishinonin Jihohi za su taka, inda ya ce su ne za su sauke hangen nesa na kungiyar zuwa kowace jiha, ƙaramar hukuma da kuma gunduma.

 

Ya bayyana cewa aikinsu ya haɗa da tara mambobi, kafa tsare-tsare masu haɗa kowa da kowa, da tabbatar da cewa mata, matasa, tsofaffi da kuma masu nakasa sun samu wakilci a kowane reshe na jihohi.

 

Ya ƙara da cewa nadin kwamishinonin jihohi zai ɗauki watanni 12 a matsayin gwaji, daga bisani kuma nagarta da sadaukarwa za su tantance sahihancin mukamansu.

 

Yayin kaddamar da kwamitoci da kwamishinonin, Dr. Idris ya tunatar da su cewa an zaɓe su ne bisa ƙwarewa, gaskiya da sadaukarwa, ba saboda sa’a ba.

 

Ya shawarce su da su gudanar da aikinsu cikin gaskiya, tawali’u da ladabi, yana mai jaddada cewa nasarar kungiyar ta dogara da yadda za su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

 

COV: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara