Connect with us

Labarai

Ana Shirin Kaddamar da Sabon Shirin Karatu Kan Cutuka Masu Yaduwa

Published

on

Cibiyar Kasa ta Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa ta bayyana shirin kaddamar da wani sabon shirin karatu domin kara inganta kwarewar ma’aikatan lafiya wajen yaki da cututtuka masu yaduwa.

Babban Daraktan cibiyar, Dakta Abdullahi Aminu Dalhatu, ya bayyana hakan a wajen rufe taron bitar tsara manhajar karatun National Diploma a fannin cututtuka masu yaduwa da alluran rigakafi, da aka gudanar a Zariya.

Ya ce a baya ana koyar da wannan fanni ne a matakan difloma na gaba da kuma kwasa-kwasan takardar shaida, lamarin da ya bar gibi a matakan ma’aikatan lafiya na tsaka-tsaki.

A cewarsa, sabon shirin zai bai wa dalibai ilimi da kwarewar gano cututtuka, hanyoyin kariya da kuma yadda za a kula da su.

Dakta Dalhatu ya kara da cewa cututtuka masu yaduwa na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar jama’a a Najeriya da sauran kasashe masu zafi.

Shi ma Sakatare na Hukumar Ilimin Fasaha ta Kasa NBTE, Farfesa Idris Muhammad Bugaje, ya ce shirin zai taimaka wajen karfafa horas da kwararrun ma’aikatan lafiya a Najeriya.

Masana da suka halarci bitar sun kuma ba da shawarar a fara aiwatar da shirin a kalla a wata cibiyar kafin karshen shekarar nan.

 

Ibrahim Suleiman/Zaria

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara