Labarai
Ana Shirin Kaddamar da Sabon Shirin Karatu Kan Cutuka Masu Yaduwa
Cibiyar Kasa ta Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa ta bayyana shirin kaddamar da wani sabon shirin karatu domin kara inganta kwarewar ma’aikatan lafiya wajen yaki da cututtuka masu yaduwa.
Babban Daraktan cibiyar, Dakta Abdullahi Aminu Dalhatu, ya bayyana hakan a wajen rufe taron bitar tsara manhajar karatun National Diploma a fannin cututtuka masu yaduwa da alluran rigakafi, da aka gudanar a Zariya.
Ya ce a baya ana koyar da wannan fanni ne a matakan difloma na gaba da kuma kwasa-kwasan takardar shaida, lamarin da ya bar gibi a matakan ma’aikatan lafiya na tsaka-tsaki.
A cewarsa, sabon shirin zai bai wa dalibai ilimi da kwarewar gano cututtuka, hanyoyin kariya da kuma yadda za a kula da su.
Dakta Dalhatu ya kara da cewa cututtuka masu yaduwa na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar jama’a a Najeriya da sauran kasashe masu zafi.
Shi ma Sakatare na Hukumar Ilimin Fasaha ta Kasa NBTE, Farfesa Idris Muhammad Bugaje, ya ce shirin zai taimaka wajen karfafa horas da kwararrun ma’aikatan lafiya a Najeriya.
Masana da suka halarci bitar sun kuma ba da shawarar a fara aiwatar da shirin a kalla a wata cibiyar kafin karshen shekarar nan.
Ibrahim Suleiman/Zaria
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai7 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
