Labarai
Ana Shirin Kaddamar da Sabon Shirin Karatu Kan Cutuka Masu Yaduwa
Cibiyar Kasa ta Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa ta bayyana shirin kaddamar da wani sabon shirin karatu domin kara inganta kwarewar ma’aikatan lafiya wajen yaki da cututtuka masu yaduwa.
Babban Daraktan cibiyar, Dakta Abdullahi Aminu Dalhatu, ya bayyana hakan a wajen rufe taron bitar tsara manhajar karatun National Diploma a fannin cututtuka masu yaduwa da alluran rigakafi, da aka gudanar a Zariya.
Ya ce a baya ana koyar da wannan fanni ne a matakan difloma na gaba da kuma kwasa-kwasan takardar shaida, lamarin da ya bar gibi a matakan ma’aikatan lafiya na tsaka-tsaki.
A cewarsa, sabon shirin zai bai wa dalibai ilimi da kwarewar gano cututtuka, hanyoyin kariya da kuma yadda za a kula da su.
Dakta Dalhatu ya kara da cewa cututtuka masu yaduwa na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar jama’a a Najeriya da sauran kasashe masu zafi.
Shi ma Sakatare na Hukumar Ilimin Fasaha ta Kasa NBTE, Farfesa Idris Muhammad Bugaje, ya ce shirin zai taimaka wajen karfafa horas da kwararrun ma’aikatan lafiya a Najeriya.
Masana da suka halarci bitar sun kuma ba da shawarar a fara aiwatar da shirin a kalla a wata cibiyar kafin karshen shekarar nan.
Ibrahim Suleiman/Zaria
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
