Connect with us

Labarai

Ana Sa-In-Sa Tsakanin NUJ Da Tsohon Shugaban NLC A Jihar Kabi

Published

on

Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ reshen jihar Kebbi, ta yi watsi da ikirarin da tsohon shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), AbdulWaheed Ibrahim Umar ya yi na cewa kafafen yada labarai na rashin bayar da rahoton irin nasarorin da al’ummar Kebbi da gwamnatin jihar suka samu.

A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Alhaji Kabiru Wurma ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, ya bayyana kalaman Umar a matsayin yaudara da kuma wani yunkuri na burge Gwamna Nasir Idris a yayin jawabin da ya yi a kungiyar NLC a jihar.

Wurma ya ce, “Mun yi matukar ba mu mamaki a lokacin da Kwamared Umar a lokacin da yake fadar shugaban kasa ya yi ikirarin cewa ya zagaya jihar domin tabbatar da nasarorin da Gwamna Idris ya samu cikin shekaru uku kacal.

Shugaban kungiyar ta NUJ ya kara jaddada irin goyon bayan da Gwamna Idris ya samu daga kafafen yada labarai, inda ya ce, “Babu wani gwamna a Najeriya da ya taba samun rahotannin da ake samu daga ‘yan jarida da kungiyoyin yada labarai kamar Gwamna Nasir Idris.

Ya kuma tunatar da cewa, a ziyarar da shugaban NLC na yanzu, Joe Ajero ya kai jihar Kebbi a ranar 23 ga Oktoba, 2024, ya yaba wa gwamnan, inda ya ce, “Babu ranar da labarai masu kyau ba sa fitowa daga jihar Kebbi.

Shugaban kungiyar ya kuma yi tambaya kan dalilin da ya sa tsohon shugaban NLC din zai yi ikirarin a kan al’amuran da ba shi da masaniya a kai, yana mai cewa babu wani aiki daya da ‘yan jarida ba su kama ko su yi aiki ba a jihar.

REL/ SANI DUTSINMA

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara