Connect with us

Labarai

An Kashe Jagoran Harin NDA Da Sace Daliban Birnin Yauri

Published

on

Sojoji sun kashe kasurgumin dan bindiga, Boderi, wanda ya kitsa harin da aka kai makarantar horas da sojoji ta NDA da ke Kaduna.

Boderi ne kuma ya kitsa hari da kuma sace dalibai a Jami’ar Greenfield da ke jihar, da kuma ’yan matan makarantar sakandaren Birnin Yauri da ke Jihar Kebbi, kamar yadda kakakin rundunar, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu, ya sanar.

Sanarwar ta ce cewa a ranar Laraba aka kashe Boderi ne tare da wani shugaban ’yan bindiga mai suna Bodejo a kan hanyar Bada–Riyawa da ke kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.

“Majiyoyin leken asiri sun ba da rahoton cewa an kashe kasurgumin dan bindiga Boderi wanda ya kitsa sace daliban Birnin Yauri, Jami’ar Greenfield da kuma NDA, tare da wani mai suna Bodejo.

“Ana ci gaba da kokarin tabbatar da hakan ta hanyar amfani da wasu hanyoyi,” in ji sanarwar.

A cewarsa, kun kwato babura 19 da ’yan ta’addan suka gudu suka bari da wasu abubuwa, kuma an kona su.

a wani samame na daban da sojoji suka kai a yankin, “’yan ta’addan da suka yi amfani da shanu a matsayin garkuwa, sun bude musu wuta, amma suka mayar da martani cikin gaggawa.

“A yayin musayar wutar ta kusan awa daya, sojoji sun kashe biyu daga cikin ’yan ta’addan tare da kwato bindiga kirar AK 47 guda 1, da sauran abubuwa.

“Sai dai kuma an kashe wasu daga cikin dabbobin satan da da ’yan ta’addan ke amfani da su a matsayin garkuwa.

“Sojoji na ci gaba da bin diddigin ’yan ta’addan da suka tsere da kuma aikinsu na samar da tsaro a yankin.”

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara