Connect with us

Kasuwanci

An Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Kaddamar Da Aikin Hanyar Firji Da Ta Ratsa Mazabu Bakwai

Published

on

An bayyana kaddamar da aikin hanyar Firji zuwa Guntai zuwa Buntusu ta wuce zuwa Dan Abzin mai nisan kilomita 29 da Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa yayi a matsayin wani muhimmin ci gaba da aka dade ana daku a yankin.

Dan majalisar dokokin jihar Jigawa Mai wakiltar mazabar Gwiwa, Alhaji Aminu Zakari ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a Gwiwa.

A cewar sa, al’ummar karamar hukumar Gwiwa za su dade su na tunawa da gwamnatin Umar Namadi bisa kaddamar da aikin wannan hanyar wacce za ta ratsa mazabu bakwai ta kuma hadu da karamar hukumar Ingawa ta jihar Katsina.

Ya kuma bayyana cewar manoma da ‘yan kasuwa na shan wahala shekara da shekaru musamman a yankunan Guntai da Buntusu wajen isa kasuwanni saboda matsalar hanya.

Alhaji Aminu Zakari ya bayyana amannar cewar idan aka kammala ta, wannan hanyar za ta bawa jama’ar mazabu bakwai damar kewayawa garuruwan yankin cikin sauki domin cin kasuwa da zuwa asibiti da ma sada zumunci.

Da ya ke tsokaci dangane da taron Gwamnati da Jama’a da Gwamna Umar Namadi ya jagoranta, Aminu Zakari ya ce taron ya kasance na kafa tarihi bisa la’akari da muhimman abubuwan da su ka wakana kamar na kaddamar da aikin hanyar Firji da hanyar burji da Kuma gyaran asibitin Gwiwa da karamar hukuma ta yi.

Kazalika, Dan Majalisar ya godewa Gwamna Namadi da mataimakin sa da shugaban majalisar dokoki da sakataren gwamnati da shugabannin jam’iya da sauran masu ruwa da tsaki bisa kasancewa tare da al’ummar karamar hukumar Gwiwa a ranar taron.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara