Kasuwanci
An Horar Da Manoma 41 Kan Noman Kayan Lambu A Kano
Wata Kungiya mai zaman kanta (NGO) ta da ake kira Netherland African Business Council (NABC) a turance, ta ce ta horar da manoma 41 kan noman kayan lambu don bunkasa wadatar abinci a jihar Kano.
Babban Jami’ar ayyukan kungiyar Hajiya Fauziyya Sadiq ta bayyana haka a wajen rufe taron horar da manoma na tsawon mako 16 a Kano.
Ta bayyana cewa horon na da nufin bunkasa aikin gona da masu zaman kansu a fannin noma a Najeriya.
A cewarta, jigon shirin na masu horas da manoman shi ne don inganta kwarewar kwararru, wadanda suka hada da wakilan kamfanonin da dillalan kayan lambu.
“An horar da manoman ta hanyar yanar gizo da kuma a fili akan ayyukan noma da taki da ban ruwa da kare amfanin gona da sauransu,” in ji ta.
Da take jawabi a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Fatima Muhammad ta yabawa hukumar ta NBC bisa wannan karimcin.
“Hakika wannan babban ci gaba ne. Mun sami sabon ilimi kan noman kayan lambu don haɓaka samar da kayan lambu,”
Ta yi alkawarin ba da ilmin da aka samu daga horon zuwa ga al’ummarsu.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, kungiyar ‘yan kasuwan Afrika ta Netherland (NABC) ce ta shirya wannan horon karkashin jagorancin Wageningen Plant Research.
KHADIJAH ALIYU/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
