Connect with us

Kasuwanci

An Horar Da Manoma 41 Kan Noman Kayan Lambu A Kano

Published

on

Wata Kungiya mai zaman kanta (NGO) ta da ake kira Netherland African Business Council (NABC) a turance, ta ce ta horar da manoma 41 kan noman kayan lambu don bunkasa wadatar abinci a jihar Kano.

 Babban Jami’ar ayyukan kungiyar Hajiya Fauziyya Sadiq ta bayyana haka a wajen rufe taron horar da manoma na tsawon mako 16 a Kano.

 Ta bayyana cewa horon na da nufin bunkasa aikin gona da masu zaman kansu a fannin noma a Najeriya.

 A cewarta, jigon shirin na masu horas da manoman shi ne don inganta kwarewar kwararru, wadanda suka hada da wakilan kamfanonin da dillalan kayan lambu.

 “An horar da manoman ta hanyar yanar gizo da kuma a fili akan ayyukan noma da taki da ban ruwa da kare amfanin gona da sauransu,” in ji ta.

 Da take jawabi a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Fatima Muhammad ta yabawa hukumar ta NBC bisa wannan karimcin.

 “Hakika wannan babban ci gaba ne. Mun sami sabon ilimi kan noman kayan lambu don haɓaka samar da kayan lambu,”

 Ta yi alkawarin ba da ilmin da aka samu daga horon zuwa ga al’ummarsu.

 Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, kungiyar ‘yan kasuwan Afrika ta Netherland (NABC) ce ta shirya wannan horon karkashin jagorancin Wageningen Plant Research.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara