Connect with us

Ilimi

An Haramta Fina-Finai Na Faɗan Daba Da Harkar Daudu A Kano

Published

on

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Kano ce ta ɗauki wannan mataki biyo bayan korafe-korafen da al’umma ke yi a kan shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a jihar.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a Yammacin wannan Larabar.

Sanarwar ta ambato Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya ba da umarnin dakatarwa tare da hana dukkan fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a faɗin jihar jim kaɗan bayan wata ganawa da ya yi da manyan ma’aikatan hukumar.

Aminiya ta ruwaito cewa, ganawar Shugaban hukumar tace fina-finan ta haɗa da wasu daga cikin wakilan ’ya’yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood ciki har da kungiyoyin MOPPAN, Arewa Film Makers, Darektoci da Furodusoshi.

Abba El-Mustapha ya ce “doka ce ta ba wa hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani fim da take ganin ya ci karo da tarbiya da al’adar al’ummar Kano.

“Saboda haka tuni lokaci ya shige da za a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su ci gaba da yaduwa a cikin al’umma.

Abba El-Mustapha ya kuma gode wa ’yan masana’antar Kannywood dangane da haɗin kai da kuma goyan bayan da suke ba wa hukumar a koda yaushe.

“Ina kuma gode wa al’ummar Jihar Kano kan irin haɗin kan da suke ba wa Hukumar musamman wajen sanar da ita duk wani abu da suke ganin ya saba da al’ada da tarbiyar addinin musulunci.

Abba El-Mustapha ya kuma yi alkawarin ci gaba da barin kofarsa a buɗe domin karɓar shawarwari ga duk wanda suke da buƙatar hakan.

A ƙarshe ya ba wa masu shirya irin wannan fina-finai na faɗan daba ko harkar daudu damar wata ɗaya da su gyara ayyukansu kafin dokar ta fara aiki gadan-gadan a kansu.

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara