Ilimi
An Haramta Fina-Finai Na Faɗan Daba Da Harkar Daudu A Kano

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Kano ce ta ɗauki wannan mataki biyo bayan korafe-korafen da al’umma ke yi a kan shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a jihar.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a Yammacin wannan Larabar.
Sanarwar ta ambato Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya ba da umarnin dakatarwa tare da hana dukkan fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a faɗin jihar jim kaɗan bayan wata ganawa da ya yi da manyan ma’aikatan hukumar.
Aminiya ta ruwaito cewa, ganawar Shugaban hukumar tace fina-finan ta haɗa da wasu daga cikin wakilan ’ya’yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood ciki har da kungiyoyin MOPPAN, Arewa Film Makers, Darektoci da Furodusoshi.
Abba El-Mustapha ya ce “doka ce ta ba wa hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani fim da take ganin ya ci karo da tarbiya da al’adar al’ummar Kano.
“Saboda haka tuni lokaci ya shige da za a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su ci gaba da yaduwa a cikin al’umma.
Abba El-Mustapha ya kuma gode wa ’yan masana’antar Kannywood dangane da haɗin kai da kuma goyan bayan da suke ba wa hukumar a koda yaushe.
“Ina kuma gode wa al’ummar Jihar Kano kan irin haɗin kan da suke ba wa Hukumar musamman wajen sanar da ita duk wani abu da suke ganin ya saba da al’ada da tarbiyar addinin musulunci.
Abba El-Mustapha ya kuma yi alkawarin ci gaba da barin kofarsa a buɗe domin karɓar shawarwari ga duk wanda suke da buƙatar hakan.
A ƙarshe ya ba wa masu shirya irin wannan fina-finai na faɗan daba ko harkar daudu damar wata ɗaya da su gyara ayyukansu kafin dokar ta fara aiki gadan-gadan a kansu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
