Labarai
An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
Gidan Talbijin na Jihar Jigawa wato JTV, ya fara gudanar da gyare-gyaren doguwar eriyar yada shirye-shiryen tashar dake garin Andaza.
Da yake yiwa shugaban gidan Talabijin na JTV Alhaji Abba Tukur karin bayani kan fara aikin, jagoran tawagar injiniyoyin, Injiniya Obi Onya, ya ce za su gudanar da aikin ta hanyar gano sassan doguwar eriyar da suke da matsala.

Injiniya Onya ya bayyana cewar, haka kuma za su gudanar da irin wannan aikin a kananan tashoshin yada shirye-shiryen tashar dake garuruwa 3 na kananan hukumomi a Jihar.

Yana mai cewar, garuruwan su ne Gumel da Hadejia da kuma Kazaure.


Shugaban gidan talabijin din wanda ya sami wakilcin Manajan Sashin injiniya na JTV, Malam Sha’aban Abubakar Tahir, ya yi bayani kan muhimmancin yi wa doguwar eriyar gyara, wanda ya ce zai karawa tashar nisan zango.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
