Ilimi
An Bukaci Ma’aurata Su Rika Neman Sani Kafin Su Fara Tara ‘Ya’ya
An bukaci ‘yan Najeriya da su halarci zaman nasiha kafin rungumar aikin tarbiyyar yara domin samun nasarar samun iyali.
Wata kwararriyar kare hakkin yara kuma mai bada shawarwari akan harkokin rayuwa, Misis Gbemisola Osagede-Daramola ta yi wannan kiran yayin da take zantawa da manema labarai a Ilorin.
A cewarta akwai basirar tarbiyyar da ma’aurata ke bukata kafin su karbi aikin tarbiyyar yaran da zasu haifa
Ta bayyana cewa galibin ma’aurata da iyaye ba sa fahimtar aikin nasiha da horar da ’yan uwansu kafin su yi tsalle cikin harkokin auratayya.
Daramola ta jaddada bukatar kafa makarantar koyar da tarbiyyar yara domin koyar da matasa ma’aurata abubuwan da suka shafi tarbiyyar yara.
Ta shawarci ma’aurata da su rika zuwa neman shawarwari kafin aure kafin su shiga tarbiyyar yara, ta kara da cewa ba za a iya koyan irin wadannan abubuwan ta hanyar bincike na google ba.
Masaniyar kare hakkin yara ta bukaci iyaye da su samar da lokaci ga ’ya’yansu, maimakon ba da fifiko ga sana’o’insu.
Ta kuma yi kira ga iyaye su daidaita harkokinsu na yau da kullum da tarbiyyar ‘ya’yansu da tarbiyyar da ta dace.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
