Ilimi
An Bukaci Ma’aikatun Gwamnati Su Rika Yin Kasafin Da Zai Amfani ‘Yan Nijeriya
Kungiyar masu ruwa da tsakin masana’antu a fannin mai ta Najeriya NEITI da hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, na kokarin kwato kusan dala biliyan shida da kuma wani naira biliyan 66 da gwamnatin tarayya ke bin gwamnatin tarayya bashin.
Sakataren zartarwa na hukumar Mista Orji Ogbonnaya Orji, wanda ya bayyana haka a lokacin kare kasafin kudin 2025 a gaban kwamitin majalisar kan albarkatun man fetur.
Mista Orji Ogbonnaya, ya bayyana cewa tuni hukumar ta gabatar da dukkan rahotannin da ta ke a masana’antar hako mai ga majalisar a wani bangare na matakan tabbatar da samun nasarar kwato kudade daga hukumomin gwamnati.
Ya ce wasu daga cikin abubuwan da hukumar ta sa a gaba a shekarar 2025 sun hada da gudanar da rahoton masana’antu na fannin iskar gas da ma’adinai, da tantance kudaden da doka ta tanada, bincike kan ainihin adadin gidaje mai da ake amfani da su a Najeriya, da kuma aiwatar da binciken ra’ayi jama’a na kasa.
Sakataren zartarwa, ya bayyana cewa NEITI a matsayin hukumar da aka kafa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkar man fetur da iskar gas a Najeriya ciki har da bangaren ma’adinai, ta sami kasafin kudin shekarar 2025 na Naira biliyan 6.5.
A nasa jawabin shugaban kwamitin kula da albarkatun man fetur na majalisar Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ya jaddada muhimmiyar rawar da hukumar ta ke takawa a fannin man fetur, ya kuma ba da tabbacin cewa kwamitin a shirye yake na mara masa baya wajen gudanar da ayyukansa.
Alhaji Alhassan Doguwa, ya shawarci shugabannin hukumar da su ci gaba da sa kaimi ga jin dadin ‘yan Nijeriya a duk lokacin da suke shirya kasafin kudin shekara bisa la’akari da yanayin tattalin arzikin da talakawa ke fuskanta daga sassa daban-daban na kasar nan.
COV: TSIBIRI/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
