Labarai
An Bukaci Gwamnoni Su Yi Koyi Da Gwamnatin Neja Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
An shawarci gwamnonin jihohin Arewa da su yi koyi da gwamnatin jihar Neja wajen magance matsalolin rikicin makiyaya da manoma a yankin domin samun ci gaba mai dorewa.
Shugaban kungiyar Miyetti Allah ta kasa MACBAN, Dokta Baba Usman Ngelzarman ne ya bayar da wannan shawarar a wajen wani taro na musamman na karramawa tare da tabbatar da lakabin gargajiya ga wasu fitattun Fulani guda biyu a jihar Neja, da aka gudanar a fadar Sarkin Minna.
Dokta Baba Usman Ngelzarman ya bayyana cewa, hanyar da Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ya bi na samar da sakamako mai kyau, ta yadda za a rage yawan rikicin makiyaya da manoma a jihar abin a yaba ne matuka.
A cewarsa hakan ya sanya bangarorin 2 sun kara fahimta da mutunta juna, wanda ya haifar da karuwar kudaden shiga a jihar da ma Najeriya baki daya.
Mai martaba Sarkin Minna Dr Umar Faruk Bahago, ya jaddada bukatar masu rike da mukaman gargajiya a yankinsa su rika gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, ta hanyar yin adalci ga kowa, don samun nasara.
A nasa jawabin sabon Jauro Minna kuma Kwamishinan kula da harkokin Makiyaya da kiwo na jihar Neja, Umar Ahmed Rebe ya yi alkawarin kara himma wajen inganta alakar manoma da makiyaya, wadda za ta ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da walwala domin samun kyakkyawan sakamako.
A nashi jawabin, Wakilin Fulanin Minna, Alhaji Hassan Usman Shiroro, ya yi kira ga Fulanin jihar Neja da su ci gaba da zama lafiya da kowa domin bunkasa ci gaban jihar Neja cikin hanzari, yana mai jaddada cewa zaman lafiya shi ne abin da ake bukata na duk wani ci gaba mai ma’ana.
Daga Aliyu Lawal
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
