Labarai
Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka
Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana ƙungiyar a matsayin ƙungiyar ta’addanci ta hanyar gabatar da wata doka.
Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Baba Usman Ngelzarma, ne ya bayyana wannan suka yayin wani taron manema labarai da aka shirya a Abuja domin nuna damuwar ƙungiyar kan wannan mataki.
Shugaban ƙungiyar ya ƙi amincewa da matakin, yana mai cewa yana zubar da mutunci da kima ta wata ƙungiya ta ƙasa da aka yi wa rajista bisa doka.
Ya jaddada cewa MACBAN ba ta goyon baya, ba ta karɓa, ba ta ɓoye, ba ta ɗaukar nauyin kuɗi, kuma ba ta kare kowanne nau’in aikata laifi, tsattsauran ra’ayi ko tashin hankali a ƙasar nan. Ya ƙara da cewa ƙungiyar na ci gaba da jajircewa wajen inganta zaman lafiya da bin doka da oda a tsakanin mambobinta.
Baba Usman ya ce, a fahimtar MACBAN, irin wannan mataki daga Majalisar Dokokin Amurka zai kawo cikas ga ƙoƙarin da ake yi na tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan ƙasa, yana mai ƙara da cewa MACBAN ba ta taɓa kasancewa ƙungiyar ɗauke da makamai ko ƙungiyar tashin hankali ba.
Ya kuma tabbatar da cewa MACBAN ta yi Allah-wadai da ayyukan fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane, ta’addanci da duk wani nau’in aikata laifi a Nijeriya, tare da yin Allah-wadai da su da kakkausar murya.
Shugaban ƙungiyar ya bayyana cewa MACBAN ƙungiya ce da gwamnatin tarayyar Nijeriya ta yi wa rajista a hukumance a matsayin ƙungiyar masu samar da dabbobi da sauran masu ruwa da tsaki a sashen kiwon dabbobi.
Ya ƙara da cewa MACBAN na nan daram kan ƙudurin ta na kare haɗin kan ƙasa, bin tsarin mulki, zaman lafiya tsakanin al’umma, bunƙasa sashen kiwon dabbobi, da kuma cikakken haɗin kai da hukumomin tsaron Nijeriya wajen yaƙi da aikata laifuka.
Ya ce: “Muna roƙon Gwamnatin Tarayya cikin girmamawa da ta kare sahihai da halastattun cibiyoyin Nijeriya daga ayyana su ba bisa ƙa’ida ba a ƙasa da ƙasa, tare da tabbatar da cewa ’yan ƙasa masu bin doka da ke samar da mafi yawan sinadarin furotin na dabbobi a Nijeriya ba a wulakanta su ko cutar da tattalin arzikinsu ba.”
Ya kuma tabbatar da cewa tun daga farkon waɗannan zarge-zarge, MACBAN ta aike da wasiƙu da dama zuwa ga manyan masu ruwa da tsaki, ciki har da ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro na Ƙasa, Shugaban Majalisar Dattawa da Ma’aikatar Harkokin Waje, domin neman shiga tsakani da gwamnatin Amurka.
A ƙarshe, MACBAN ta yi kira cikin girmamawa ga Shugaban Majalisar Dattawa da Majalisar Dokoki ta Ƙasa da su ɗauki matakin doka domin kare mutunci da martabar cibiyoyin Nijeriya. Ƙungiyar ta kuma jaddada amincewarta da ƙudurin Majalisar Dokoki na kare ƙungiyoyin Nijeriya da aka yi wa rajista daga ayyana su ba bisa adalci ba a ƙasashen waje.
Cov/Bashir Mayere
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
