Connect with us

Ilimi

Al’ummar Musulmi Sun Yi Addu’a Ta Musamman Ga Gwamna Kefas

Published

on

 

Al’ummar musulmin jihar Taraba sun gudanar da karatun kur’ani mai tsarki tare da gudanar da addu’o’i na musamman ga gwamna Agbu Kefas da al’ummar jihar Taraba.

 

An gudanar da addu’ar ce a masallacin Juma’a na Saurara da ke Jalingo, babban birnin jihar a ranar Asabar 4 ga watan Janairu, 2025.

 

An fara shirin ne da karatun kur’ani mai tsarki, sannan aka gudanar da addu’o’i na musamman karkashin jagorancin manyan limamai na wasu masallatan Juma’a na jihar.

 

A karkashin jagorancin Malam Hussaini Isma’ila, mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin addinin musulmi, taron ya hada manyan limamai da malaman addinin musulunci daga kananan hukumomin jihar 16.

 

Malaman addinin Islama sun nuna godiyarsu ga Gwamna Agbu Kefas bisa namijin kokarin da yake yi na gina babbar jihar Taraba ga kowa da kowa.

 

A cikin addu’o’in da suka yi, malamai sun roki Allah ya ci gaba da yi masa jagora, ya ba shi lafiya, da nasara mai dorewa ga Gwamna da tawagarsa.

 

Malam Hussaini Ismaila, mai baiwa gwamna Agbu Kefas shawara kan harkokin addinin musulmi, ya karkare taron da kira ga ‘yan uwa musulmi na jihar Taraba da su hada kai da goyon bayan gwamnatin Gwamna Kefas.

 

Taron addu’o’i na musamman da Malam Hussaini Isma’ila ya shirya ya nuna kyakykyawar alaka tsakanin al’ummar Musulmi da gwamnatin Gwamna Agbu Kefas a halin yanzu, da kuma sadaukarwar da suke yi na samar da zaman lafiya da hadin kai da ci gaba.

 

 

Sani Sulaiman/Wababe

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara