Connect with us

Labarai

Al’ummar Jigawa Sun Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Shirin Ciyarwa Na Watan Ramadan

Published

on

 

Al’ummomin Jihar Jigawa na ci gaba da nuna jin dadinsu dangane da bullo da ciniyoyin yin bude baki a watan Ramadan.

Wasu daga cikinsu da Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya zanta da su, da suka fito daga kananan hukumomin Dutse da Ringim da Hadejia da Gumel, da kuma Kazaure, sun bayyana cewar wannan hangen nesa da Gwamnan yayi zai matukar kawo masu sauki a wannan yanayi da ake ciki na hauhawar farashin kayan abinci.

Mallam Ali Bashir Kazaure da Dahiru Dutse sun nuna gamsuwa bisa cibiyoyin da gwamnatin jihar ta kafa domin ciyar da al’umma abincin bude baki.

Suma da suke tofa albarkacin bakin su, Malama Hansatu Sidi dake karamar hukumar Ringim da Talatu Abashe dake karamar hukumar Hadejia sun bayyana godiyarsu ga Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi bisa wannan tallafin kayayyakin abinci da aka fara kaddamarwa na rabawa al’ummar jihar.

Suna mai cewar shakka babu, suna samun tagomashi daga Gwamnati bisa tallafi da ake raba wa al’umma,  musamman  a kauyaku masu wahalar shiga.

Sai dai kuma, Malam Nura Usman Gumel yayi kira ga masu hannu da shuni da kungiyoyin da ba na gwamnati ba, da su taimakawa mutane da abinci a wannan watan na ramadan mai albarka.

Ya kuma bukaci al’umma da su rika tunawa gami da taimakawa marayu da abinci da suturu, domin samun lada a wajen Allah SWT.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kayayyakin da aka raba sun hada da buhunan shinkafa da masara dubu dari uku da katan din taliya dubu dari daya.

Kazalika, Gwamnatin jihar na sa ran mutane dubu dari daya da saba’in  da tara da da dari bakwai ne za su amfana  da tallafin ciyarwar a kowace rana na tsawon wata guda a jihar.

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara