Connect with us

Kasuwanci

Al’ummar Jigawa Sun Bukaci Gwamnati Ta Yi Koyi Da Shirin NG-CARES Wajen Tallafawa Mabukata

Published

on

Al’ummar Jihar Jigawa sun yi kira ga Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi da ya yi amfani da kyawawan tsarin da gaskiya wajen zabar wadanda za su ci gajiyar shirye-shiryen bada tallafin karfafa sana’o’i.

Sun kuma bukaci gwamnatin jihar da ta yi amfani da tsarin bayar da tallafin karfafa al’umma ma gwamnatin tarayya na (FADAMA) a  dukkan shirye shiryenta ta bada tallafi,  domin ganin al’ummar jihar sun ci gajiyar ayyukan gwamnati.

Wani shugaban al’ummar yankin Walewale a karamar hukumar Garki, Malam Haruna Abdullahi, ya ce, hanyar da shirin FADAMA na gwamnatin tarayya ya yi amfani da ita ya tabbatar da cewa tallafin ya isa ga masu bukata.

A cewarsa, tsarin ya kawar da son zuciya da siyasa, wanda hakan ya  yi tasiri matuka ga al’umma.

Mun ga yadda shirin FADAMA kkarkashin shirin gwamnatin tarayya na G-CARES ya samu damar tallafawa manoma na hakika da sauran mutanen da suka cancanta, idan aka yi amfani da wannan tsari a duk wasu tsare-tsare na karfafawa, zai kawo ci gaba na hakika a jihar Jigawa.”

Wani mazaunin garin, Usman Alhaji na Arbun a karamar hukumar Auyo, ya kara da cewa daukar tsarin zaben wadanda suka cancanta zai kara wa gwamnatin jihar kima a idon  jama’a.

Sun bukaci Gwamna Namadi da ya yi amfani da wannan tsari ga sauran shirye-shiryen karfafawa a jihar, tare da tabbatar da cewa tallafin gwamnati na isa ga wadanda suka fi bukata.

Shi ma da yake jawabi, shugaban kwamitin riko na shirin FADAMA CARES, Dakta Saifullahi Umar ya bayyana cewa, shirin na NG-CARES  an tsara shi ne domin dakile matsin tattalin arzikin da annobar Corona

. ta haifar.

Dakta Saifullahi ya ce, abu na 2 wanda aka aiwatar ta hanyar shirin FADAMA, yana mai da hankali  ne kan tallafin noma da inganta rayuwa, ta hanyar yin amfani da kyakkyawan tsari wajen zabo wadanda suka dace su ci gajiyar shirin.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara