Labarai
Allah Ya Yi Wa Dan Gwamnan Jigawa Rasuwa
Allah Ya yi wa Abdulwahab Umar Namadi, dan gwamnan jihar Jigawa rasuwa.
Marigayin ya rasu ne da yammacin yau Alhamis sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar Dutse zuwa Kafin Hausa a jihar ta Jigawa.

A wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ya rabawa manema labarai a Dutse ya bayyana cewa, Marigayi Abdulwahab mai shekaru 24 ya rasu ya bar iyayensa da ’yan uwa da dama.
“Cikin alhini tare da mika wuya ga Allah, Mai Girma Gwamna Mallam Umar Namadi, na sanar da rasuwar babban dansa Abdulwahab Umar Namadi“.

Tuni aka yi jana’izar marigayin kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar, a garin Kafin Hausa.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, mahaifiyar Gwamnan, Hajiya Maryam Namadi ta rasu a jiya Laraba 25 ga watan Disamban 2024, a lokacin da yake ziyarar aiki a kasar China.

Da yammacin yau ne Gwamnan ya isa jihar Jigawa daga tafiyar.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
