Labarai
Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar 2026.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa katin rigakafin wajibi ne ga dukkan maniyyatan da za su tafi ƙasar Saudiyya domin aikin Hajji.

Alhaji Labbo wanda ya bayyana cewa jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fara kammala shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026, ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da tarukan wayar da kai da horar da maniyyata a kowace rana a dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar a cibiyoyin da aka tanadar
Ya ce nan ba da jimawa ba hukumar za ta fara raba yunifom da sauran kayayyakin tafiya ga maniyyatan 2026.

Labbo ya yaba wa ma’aikatan hukumar bisa ƙwazon su da haɗin kai wajen gudanar da ayyukansu.
Haka kuma, shugaban hukumar ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa ci gaba da ba su goyon baya da haɗin kai.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
-
Labarai7 days agoHukumar Lafiya a Kano ta Shirya Taron Masu Ruwa da Tsaki Kan Cutar Shan Inna
