Connect with us

Labarai

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Published

on

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a masallatan Juma’a da coci-coci, tare da gudanar da shirin jinya kyauta a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Farko (PHC) ta Chikaji, a ƙaramar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

Gangamin na daga cikin shirin wayar da kai domin ƙara fahimtar jama’a kan hanyoyin kariya, gano cutar da wuri, da kuma maganinta, tare da ƙarfafa shigar al’umma cikin yaki da cutar.

Da yake jawabi yayin aikin, Darakta-Janar na Cibiyar, Dakta Abdullahi Dalhatu Aminu, ya bayyana kwarin gwiwa cewa za a iya kawar da tarin fuka idan dukkan masu ruwa da tsaki suka tashi tsaye wajen yakar ta.

Ya jaddada cewa kawar da cutar na bukatar haɗin kai tsakanin gwamnati, al’umma da kuma daidaikun mutane, yana mai cewa nasara za ta samu ne idan kowa ya taka rawarsa.

Dakta Abdullahi ya bayyana cewa gwamnati na bayar da magungunan tarin fuka kyauta, tare da gwaje-gwaje da sauran hanyoyin gano cutar a sassa daban-daban na ƙasar.

Sai dai ya ce har yanzu wasu marasa lafiya na fuskantar ƙalubale wajen samun cibiyoyin lafiya sakamakon matsalar sufuri da sauran buƙatun yau da kullum.

Ya ƙara da cewa Najeriya ce ta huɗu a duniya wajen yawan masu dauke da tarin fuka, kuma ta farko a nahiyar Afirka, lamarin da ya bayyana a matsayin babban ƙalubale na lafiya da ke bukatar gaggawar magancewa.

Ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kai, tare da neman goyon bayan jama’a da hukumomi ta hanyar tallafi da shawarwari domin kawo ƙarshen cutar a Najeriya.

Haka kuma, wata kwararriyar likita, Dakta Umma Aliyu, wacce ke kula da sashen kula da marasa lafiya, ta ce tarin fuka cuta ce mai warkewa kuma mai hana yaɗuwa idan aka bi matakan kariya da suka dace.

Ta bayyana cewa kariya daga cutar na bukatar guje wa cunkoson jama’a da kuma tabbatar da samun iska mai kyau a gidaje da wuraren taruwar jama’a.

Dakta Aliyu ta kuma shawarci mutane da su guji shan taba sigari da yawan shan giya, tana mai cewa waɗannan halaye na ƙara haɗarin kamuwa da tarin fuka.

Wasu daga cikin marasa lafiyar tarin fuka da suka halarci shirin sun nuna godiya ga National Institute of Public Health and Infectious Diseases bisa shirya wannan gangamin wayar da kai.

Rahoton Radio Nigeria ya ce yayin gangamin, ƙwararru sun shafe wani ɓangare na rana a PHC Chikaji inda aka gudanar da gwaje-gwaje da shawarwari kyauta ga mutane da dama, ciki har da yara da manya.

Ibrahim Suleiman/Zaria

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara