Labarai
Kiristoci a Kwara sun fito kan titi domin bikin Palm Sunday
Dubban mabiya addinin Kirista a jihar Kwara sun fito kan tituna domin bikin Palm Sunday, ranar tunawa da shigowar Yesu Almasihu cikin birnin Urushalima cikin nasara, kamar yadda littattafan addini suka bayyana.
Bikin na kuma nuni da ƙarshen azumin kwanaki 40 na Lenten Fast da kuma fara makon ibada na Easter (Holy Week).
Mabiya addinai daga dariku daban-daban sun taru a Cocin Saint Barnabas Cathedral, Sabo-Oke, inda daga nan suka gudanar da jerin gwanon tafiya na sa’o’i da dama ta wasu muhimman titunan birnin Ilorin, ciki har da Murtala Way, Maraba, Amilegbe, Ipata, Opo-Malu, Emir’s Road, Taiwo Isale, Unity da kuma yankin Ofishin Wasiƙa, kafin daga bisani su koma cocin inda aka kammala da addu’ar rufewa (benediction).
Da yake jawabi bayan kammala jerin gwanon, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Kwara, Right Reverend Sunday Adewole, ya bukaci Kiristoci da su ci gaba da kasancewa cikin tsayuwar imani da hidima ga Allah.
Ya kuma yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, yana mai cewa tsaron jama’a ya kamata ya kasance abu na farko a fifiko.
Adewole ya kuma jaddada tasirin hauhawar farashin man fetur da ƙarancin wutar lantarki a gidaje da kasuwanci, yana mai cewa akwai bukatar gaggawar magance waɗannan matsaloli na tattalin arziki.
A nasa ɓangaren, Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, wanda wakilinsa, Reverend Timothy Akangbe, ya halarta, ya bukaci jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin ci gaban jihar da Najeriya baki ɗaya.
Ya kuma jaddada muhimmancin tawali’u da soyayya a rayuwar yau da kullum.
Tsohon Sakatare na CAN, Pa Olusola Ajolore, ya yi kira da a ɗauki matakan gaggawa wajen magance matsalar tsaro, tare da shawartar gwamnatoci su yi amfani da kuɗaɗen tsaro yadda ya kamata domin kare rayuka da dukiya.
Ya kuma bukaci samar da ayyukan yi da kuma sake duba kundin tsarin mulki domin dacewa da halin da ake ciki a yau.
Haka kuma, Babban Annabi Segun Korode na Cocin Cherubim and Seraphim Movement Church, Hedikwatar Ilorin, ya tunatar da mabiya cewa su riƙa gode wa Allah a kowane lokaci tare da koyi da tawali’un Yesu Almasihu wanda ya zo da ceton ɗan adam.
Bikin Palm Sunday a Ilorin ya nuna haɗin kai na ibada tare da ƙara jaddada kira ga al’umma kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.
Ali Muhammad Rabiu
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
