Connect with us

Labarai

Kiristoci a Kwara sun fito kan titi domin bikin Palm Sunday

Published

on

Dubban mabiya addinin Kirista a jihar Kwara sun fito kan tituna domin bikin Palm Sunday, ranar tunawa da shigowar Yesu Almasihu cikin birnin Urushalima cikin nasara, kamar yadda littattafan addini suka bayyana.

Bikin na kuma nuni da ƙarshen azumin kwanaki 40 na Lenten Fast da kuma fara makon ibada na Easter (Holy Week).

Mabiya addinai daga dariku daban-daban sun taru a Cocin Saint Barnabas Cathedral, Sabo-Oke, inda daga nan suka gudanar da jerin gwanon tafiya na sa’o’i da dama ta wasu muhimman titunan birnin Ilorin, ciki har da Murtala Way, Maraba, Amilegbe, Ipata, Opo-Malu, Emir’s Road, Taiwo Isale, Unity da kuma yankin Ofishin Wasiƙa, kafin daga bisani su koma cocin inda aka kammala da addu’ar rufewa (benediction).

Da yake jawabi bayan kammala jerin gwanon, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Kwara, Right Reverend Sunday Adewole, ya bukaci Kiristoci da su ci gaba da kasancewa cikin tsayuwar imani da hidima ga Allah.

Ya kuma yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, yana mai cewa tsaron jama’a ya kamata ya kasance abu na farko a fifiko.

Adewole ya kuma jaddada tasirin hauhawar farashin man fetur da ƙarancin wutar lantarki a gidaje da kasuwanci, yana mai cewa akwai bukatar gaggawar magance waɗannan matsaloli na tattalin arziki.

A nasa ɓangaren, Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, wanda wakilinsa, Reverend Timothy Akangbe, ya halarta, ya bukaci jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin ci gaban jihar da Najeriya baki ɗaya.

Ya kuma jaddada muhimmancin tawali’u da soyayya a rayuwar yau da kullum.

Tsohon Sakatare na CAN, Pa Olusola Ajolore, ya yi kira da a ɗauki matakan gaggawa wajen magance matsalar tsaro, tare da shawartar gwamnatoci su yi amfani da kuɗaɗen tsaro yadda ya kamata domin kare rayuka da dukiya.

Ya kuma bukaci samar da ayyukan yi da kuma sake duba kundin tsarin mulki domin dacewa da halin da ake ciki a yau.

Haka kuma, Babban Annabi Segun Korode na Cocin Cherubim and Seraphim Movement Church, Hedikwatar Ilorin, ya tunatar da mabiya cewa su riƙa gode wa Allah a kowane lokaci tare da koyi da tawali’un Yesu Almasihu wanda ya zo da ceton ɗan adam.

Bikin Palm Sunday a Ilorin ya nuna haɗin kai na ibada tare da ƙara jaddada kira ga al’umma kan zaman lafiya, tsaro da ci gaban tattalin arziki.

Ali Muhammad Rabiu

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara