Connect with us

Fasaha

Za a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin Najeriya – Nimet

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakan kare lafiya ba, to akwai yiyuwar mazauna Abuja, Kano, da sauran jihohin Arewa da dama za su fuskanci tsananin zafi wanda zai shafi lafiyarsu.

Tsananin zafi dai na janyo cutuka da dama waɗanda za su iya kai wa mutuwa, kuma hakan a faruwa ne a lokacin da jiki ya kasa sarrafa zafin.

Mazauna waɗannan jihohin na iya fuskantar matsanancin zafi, wanda zai sa su shiga yanayi mara kyau, a cewar Nimet.

“Mun sake shiga lokacin zafi. Ya kamata jama’a su ɗauki matakan da suka dace,” kamar yadda “NiMET ta yi gargaɗi.

Ta ce Abuja, Kano, Sokoto, da Kogi ne za su fi fuskantar tsananin zafi, inda ta shawarci mazauna yankunan da su ɗauki matakin kariya da ya kamata.

Wasu jihohin da ke cikin rukunin fuskantar zafin sun haɗa da Kebbi, Katsina, Adamawa, Gombe, Bauchi, Taraba, Neja, Zamfara, Nasarawa, Jigawa, Benue, da kuma Kwara.

NiMET ta kuma gargaɗi mazauna jihohin Osun, Ekiti, Ondo, Bayelsa, Akwa Ibom, Anambra, Delta, Enugu, Edo, Ogun, Plateau, Borno, Imo, Abia, da Cross River da cewa su kasance cikin shiri don karuwar zafi, duk da cewa zafin ba zai yi tsanani ba kamar na sauran jihohi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai13 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai14 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai15 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi16 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara