Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana

Published

on

Daga Usman Mohammed Zaria

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kaddamar da kwamitin Amirul Hajj na bana karkashin jagorancin Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Hameem Nuhu Muhammadu Sanusi.

A Jawabin sa wajen kaddamar da kwamitin, Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce tuni hukumar Alhazai ta jihar ta kammala duk wani shiri da yakamata domin tunkarar aikin hajjin bana.

Yana mai cewar sun samar da masaukai ga maniyyata a kusa da harami kuma masu inganci, yayin da ake ci gaba da bita ga maniyata domin ilmantar da su dokokin aikin hajji.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce a bana hukumomin Saudiya sun fito da tsarin cewar sai maniyaci yana da koshin lafiya za’a bari ya sauke farali.

Alhaji Ahmed Labbo, ya kuma bayyana cewar a bara hukumar ta samu lambobin yabo sakamakon ficen da tayi a aikin hajjin 2025. Yana mai fatan a bana za’a samu karin lambobin yabo a yayin gudanar da aikin hajjin.

A jawabinsa, Amirul hajjin kuma mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Hameem Muhammadu Sunusi ya bada tabbacin yin duk abin da ya dace domin samun nasarar gabatar da aikin hajjin bana.

Kazalika, ya kuma yi fatan kwamitin zai yi aiki tare da ma’aikatan hukumar domin samun nasarar da ake bukata, kasancewar Darakta janar na hukumar kwararre ne a wannan aiki.

 

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara