Connect with us

Labarai

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Published

on

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma samun magani kyauta kan cutar Glaucoma ko kuma dundumi, a wani bangare na bukukuwan Ranar Glaucoma ta Duniya ta bana.

Da take jawabi a wajen shirin, ƙwararriyar likitar ido a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos Farfesa Perpetua Udogbo, ta bayyana cewa jami’an FRSC na iya taka muhimmiyar rawa wajen rage hadurran mota a kan tituna ta hanyar tabbatar da cewa direbobin da ke tuka ababen hawa suna da lafiyayyen gani.

Wakilinmu Josiah Buzun ya ruwaito cewa an gudanar da gwajin ne a hedikwatar FRSC da ke kan titn Zaria a Jos, da kuma ofishin su na Bukuru, domin sauƙaƙa wa mahalarta samun damar halartar shirin.

Shirin wani bangare ne na ayyukan da ake gudanarwa domin bikin Makon Glaucoma na Duniya, wanda ƙungiyar Sight Savers International ta dauki nauyi tare da haɗin gwiwar Health and Development Support Programme (HANDS), Christian Blind Mission, da kuma Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Filato.

Ko da yake an shirya gwajin ne musamman ga jami’ai da ma’aikatan FRSC, wasu mazauna yankin sun kuma yi amfani da damar domin a duba idanuwansu domin gano ko suna dauke da cutar.

Farfesa Udogbo ta yi kira ga a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da FRSC domin tabbatar da cewa direbobin da ke tuka ababen hawa a kan tituna suna da lafiyayyen gani kafin a ba su damar yin tuƙi.

Ta kuma jaddada muhimmancin yin gwajin cutar da wuri domin gano ta da kuma fara magani cikin lokaci, tana mai cewa Glaucoma cuta ce mai hatsari wadda kan iya janyo makanta a lokacin da mutum ke cikin shekarun aiki, lamarin da kan rage ingancin rayuwa tare da haddasa matsin lamba a zuciya.

Farfesa Udogbo ta bayyana cutar Glaucoma a matsayin irin hawan jini na ido, inda matsin da ke cikin ido ke karuwa har ya iya lalata jijiyoyin gani.

Sai dai ta ce idan an gano cutar da wuri, ana iya rage matsin da ke cikin ido ta hanyar magunguna, amfani da wasu kwayoyi ko kuma yin tiyata.

Mukaddashin Shugaban Kwamitin Lafiyar Ido na Jihar Filato, Dakta Rwang Pam Haruna, ya ce sun zabi gudanar da wannan gwaji ga jami’an FRSC ne saboda muhimmiyar rawar da suke takawa wajen tabbatar da tsaron hanya.

Shi ma Kwamandan Yanki na FRSC ya yaba da wannan shiri, yana mai cewa wani muhimmin mataki ne da ke taimakawa rayuwar dan Adam.

Daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a wajen taron har da yin gwajin lafiya kyauta, inda aka raba magunguna da tabarau ga wadanda aka gano suna bukata.

Josiah Buzum/Jos

Labarai

Labarai3 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai3 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai3 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai3 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai3 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara