Labarai
An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma samun magani kyauta kan cutar Glaucoma ko kuma dundumi, a wani bangare na bukukuwan Ranar Glaucoma ta Duniya ta bana.
Da take jawabi a wajen shirin, ƙwararriyar likitar ido a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos Farfesa Perpetua Udogbo, ta bayyana cewa jami’an FRSC na iya taka muhimmiyar rawa wajen rage hadurran mota a kan tituna ta hanyar tabbatar da cewa direbobin da ke tuka ababen hawa suna da lafiyayyen gani.
Wakilinmu Josiah Buzun ya ruwaito cewa an gudanar da gwajin ne a hedikwatar FRSC da ke kan titn Zaria a Jos, da kuma ofishin su na Bukuru, domin sauƙaƙa wa mahalarta samun damar halartar shirin.
Shirin wani bangare ne na ayyukan da ake gudanarwa domin bikin Makon Glaucoma na Duniya, wanda ƙungiyar Sight Savers International ta dauki nauyi tare da haɗin gwiwar Health and Development Support Programme (HANDS), Christian Blind Mission, da kuma Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Filato.
Ko da yake an shirya gwajin ne musamman ga jami’ai da ma’aikatan FRSC, wasu mazauna yankin sun kuma yi amfani da damar domin a duba idanuwansu domin gano ko suna dauke da cutar.
Farfesa Udogbo ta yi kira ga a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da FRSC domin tabbatar da cewa direbobin da ke tuka ababen hawa a kan tituna suna da lafiyayyen gani kafin a ba su damar yin tuƙi.
Ta kuma jaddada muhimmancin yin gwajin cutar da wuri domin gano ta da kuma fara magani cikin lokaci, tana mai cewa Glaucoma cuta ce mai hatsari wadda kan iya janyo makanta a lokacin da mutum ke cikin shekarun aiki, lamarin da kan rage ingancin rayuwa tare da haddasa matsin lamba a zuciya.
Farfesa Udogbo ta bayyana cutar Glaucoma a matsayin irin hawan jini na ido, inda matsin da ke cikin ido ke karuwa har ya iya lalata jijiyoyin gani.
Sai dai ta ce idan an gano cutar da wuri, ana iya rage matsin da ke cikin ido ta hanyar magunguna, amfani da wasu kwayoyi ko kuma yin tiyata.
Mukaddashin Shugaban Kwamitin Lafiyar Ido na Jihar Filato, Dakta Rwang Pam Haruna, ya ce sun zabi gudanar da wannan gwaji ga jami’an FRSC ne saboda muhimmiyar rawar da suke takawa wajen tabbatar da tsaron hanya.
Shi ma Kwamandan Yanki na FRSC ya yaba da wannan shiri, yana mai cewa wani muhimmin mataki ne da ke taimakawa rayuwar dan Adam.
Daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a wajen taron har da yin gwajin lafiya kyauta, inda aka raba magunguna da tabarau ga wadanda aka gano suna bukata.
Josiah Buzum/Jos
-
Labarai7 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai7 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai7 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai7 days agoRamadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji
-
Labarai4 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai7 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai4 days agoSojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
