Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

 Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa Cibiyar Bincike da Adana Tarihi da Al’adun Jihar Zamfara.

Farfesa Adamu ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci tawagar shugabannin jami’ar ziyarar girmamawa ga Sarkin Anka kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad.

Sanarwar da Babban Jami’in Hulɗa da Jama’a na jami’ar, Jamilu Ibrahim Gusau, ya fitar ta ce ziyarar na daga cikin jerin ganawa da masu ruwa da tsaki da  Shugaban jami’ar ke yi domin shimfiɗa alkiblar tafiyar da sabuwar gwamnatinsa.

A cewar Farfesa Adamu, cibiyar da ake shirin kafawa za ta mayar da hankali ne kan karewa, tattarawa da bunƙasa tarihin arziki da al’adun gargajiya na Jihar Zamfara.

Ya jaddada cewa wannan shiri na nuna muhimmancin da ake bai wa masarautu da kuma bukatar kare ilimin gargajiya domin amfanin al’umma masu zuwa.

Shugaban jami’ar ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi aiki kafada da kafada da Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara domin tabbatar da cewa al’ummar jihar sun amfana da damar ilimi da ci gaba a FUGUS.

Ya yi kira ga Majalisar Sarakunan da ta jagoranci ƙoƙarin ƙara yawan ɗalibai ‘yan asalin Zamfara da ke samun gurbin karatu a jami’ar, yana mai cewa faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi zai taimaka wajen hanzarta ci gaban jihar baki ɗaya.

A nasa jawabin, Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Ahmad, ya yaba wa Shugaban jami’ar da tawagarsa kan ziyarar, inda ya bayyana ta a matsayin farkon sabunta haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da masarautu.

Ya ce ƙarfafa haɗin kai zai taimaka matuƙa wajen magance ƙalubalen zamantakewa da na ci gaba a jihar.

Sarkin ya kuma bayyana cewa Majalisar Sarakunan Jihar za ta yi aiki tare da jami’ar wajen shirya taruka da bitoci ga sarakunan gargajiya, tare da habbaka gudummawar da masu sarauta ke takawa a faɗin Jihar Zamfara.

Labarai

Labarai3 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi3 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai3 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai5 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara