Connect with us

Labarai

KAROTA Ta Sha Alwashin Ƙara Ƙarfafa Haɗin Kai da Jami’an Soji a Jihar Kano

Published

on

Daga Khadijah Aliyu 

Shugaban Hukumar Kula da Hanyoyi da Tsaron Ababen Hawa ta Jihar Kano,  (KAROTA), Faisal Mahmud Kabir, ya sake jaddada kudirinsa na inganta dangantaka mai kyau da haɗin kai da rundunonin soji da ke aiki a jihar Kano.

Faisal Mahmud ya sha alwashin hakan  ne yayin da ya karɓi baƙuncin Kwamandan 403 na makarantar horar da matukan jiragen sama da ke Kano, Group Captain Uchenna Ihediwa, a hedikwatar KAROTA.

Shugaban na KAROTA  ya amince cewa a wasu lokuta ana samun rashin fahimta tsakanin jami’an KAROTA da jami’an soji, amma ya tabbatar da cewa hukumar na aiki domin samar da hanyoyin warware duk wata takaddama cikin lumana.

Ya jaddada cewa burinsu shi ne tabbatar da kyakkyawar alaƙar aiki wadda za ta amfani jami’an tsaro da kuma al’umma baki ɗaya.

A nasa jawabin, Group Captain Uchenna Ihediwa ya ce ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwar da ke akwai tsakanin KAROTA da makarantar horas da matukan jiragen sojin sama, tare da mai da hankali kan tabbatar da doka da oda a hanyoyin jihar.

Ya jaddada muhimmancin haɗin kai, ƙwarewa, da kuma tsayawa tsayin daka ga dukkan jami’an tsaro domin tabbatar da kula da zirga-zirgar ababen hawa.

Kwamandan ya yabawa jami’an KAROTA bisa jajircewarsu da ƙwazon aikinsu, inda ya nuna buƙatar ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin inganta tsaron jama’a da kuma tabbatar da bin dokokin zirga-zirga.

 

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara