Labarai
Mutane 7 Sun Mutu Sanadiyar Girgizar Kasa A Taiwan
Akalla mutane 7 ne suka mutu a girgizar kasa mafi muni ta baya-bayan da aka samu cikin shekaru 25 a Taiwan, sannan akwai wasu sama da dari 7 da suka samu raunuka.
Hukumomin kasar sun ce, jami’an bada agaji na ci gaba da aikin ceto wadanda suka makale a cikin gidaje da dama da lamarin ya shafa.

A cewar wani malamin asibiti a Taipei, Chang Yu-lin, girgizar kasar mai karfin maki 7 da 2, ta afkawa yankin Gabashin kasar ne da ke da yawan jama’a.
Girgizar da aka sameta a nisan kilomita 15.5, ta faru ne a dai-dai lokacin da mutane ke tafiya aiki da zuwa makaranta, wacce kuma ta haifar da baraznar tasowar Tsunami a kudancin Japan da kuma Philippings, duk da cewa daga baya an ce ta kauce.
Jami’an kashe gobara sun ce har yanzu akwai kimanin mutane 60 daga cikin kusan 77 da suka makale a hanyoyin karkashin kasa da ke arewacin birnin Haulien.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai24 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
