Connect with us

Labarai

Matatar Man Ɗangote Ta Fara Sayar Da Man Jirgi Da Na Dizil

Published

on

Matatar man attajirin Najeriya Aliko Dangote ta fara fitar da albarkatun man fetur din da ta tace, kamar yadda daya daga cikin manyan jami’an kula da matatar da kuma kungiyar dillalan man fetur din a Najeriya suka tabbatar.

Daga cikin manyan jami’ai a rukunonin kamfanin na Dangote Devakumar Edwin ne ya tabbatar da samun wannan ci gaba, yayin zantawa kamfanin dillancin labarai na Reuters, inda ya ce tuni suka fara rarraba wa ‘yan kasuwa man disel da kuma man jiragen sama.

 

A cewar jami’in, litar mai miliyan 37 suke fatan cimma fara dorawa manyan jiragen ruwa, amma a halin yanzu suna iya lodin litar man miliyan 26.

 

Kamfanin dillancin labaran na Reuters ya kuma ruwaito shugaban kungiyar dillalan man fetur na Najeriya Abubakar Maigandi na cewa, sun cimma matsayar sayen litar man disel daga matatar man ta Dangote kan farashin naira dubu 1,225, kwatankwacin kusan dalar Amurka guda, wanda za su rarraba zuwa sassan Najeriya.

 

Matatar man ta Dangote da ke jihar Legas ta lakume dalar Amurka biliyan 20 kafin kammala aikin gininta, wadda za ta rika tace gangar danyen mai dubu 650,000 a kowace rana, abinda yasa idan har ta fara cikakken aikin da aka tsara mata a bana ko kuma badi, matatar za ta zama mafi girma a nahiyar Afirka da ma Turai, ci gaban da ake fatan zai kawo karshe ko kuma rage dogaron da Najeriya ke yi wajen shigar da tataccen man fetur daga Turai, duk da dimbin arzikin danyen man da take da shi.

 

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai22 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai23 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai1 day ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi1 day ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara