Labarai
Mutane 7 Sun Mutu Sanadiyar Girgizar Kasa A Taiwan
Akalla mutane 7 ne suka mutu a girgizar kasa mafi muni ta baya-bayan da aka samu cikin shekaru 25 a Taiwan, sannan akwai wasu sama da dari 7 da suka samu raunuka.
Hukumomin kasar sun ce, jami’an bada agaji na ci gaba da aikin ceto wadanda suka makale a cikin gidaje da dama da lamarin ya shafa.
A cewar wani malamin asibiti a Taipei, Chang Yu-lin, girgizar kasar mai karfin maki 7 da 2, ta afkawa yankin Gabashin kasar ne da ke da yawan jama’a.
Girgizar da aka sameta a nisan kilomita 15.5, ta faru ne a dai-dai lokacin da mutane ke tafiya aiki da zuwa makaranta, wacce kuma ta haifar da baraznar tasowar Tsunami a kudancin Japan da kuma Philippings, duk da cewa daga baya an ce ta kauce.
Jami’an kashe gobara sun ce har yanzu akwai kimanin mutane 60 daga cikin kusan 77 da suka makale a hanyoyin karkashin kasa da ke arewacin birnin Haulien.
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha4 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai1 day ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai15 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert