Connect with us

Labarai

Ku Kyale Kananan Hukumomi Su Ci Gashin Kansu- Shugaba Tinubu

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya gargadi gwamnonin jihohi da su guji saba hukuncin Kotun Koli da ya bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu game da kuɗadensu, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da rashin bin hukuncin na iya jawo Gwamnatin Tarayya ta shiga tsakani.

Ya jaddada cewa dole ne a mutunta hukuncin tare da aiwatar da shi gaba ɗaya domin ƙarfafa shugabanci a matakin ƙananan hukumomi.

Shugaban ya bayar da wannan gargaɗi ne a yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) karo na 15 na jam’iyyar APC, wanda aka gudanar a Cibiyar Taro ta Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Tinubu ya nuna damuwa kan yadda wasu gwamnatocin jihohi ke ci gaba da riƙe kuɗaɗen rabon da doka ta tanada da ya kamata a bai wa ƙananan hukumomi.

Ya bayyana cewa duk da ya zaɓi nuna haƙuri da girmamawa wajen mu’amala da gwamnonin, Gwamnatin Tarayya na da ikon tilasta bin doka.

Ya yi gargaɗin cewa idan gwamnonin suka ƙi bin hukuncin, Gwamnatin Tarayya na iya fara biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga Asusun Tarayya (Federation Account), bisa tanadin kundin tsarin mulki da kuma umarnin Kotun Koli.

Labarai

Labarai2 days ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai2 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai2 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai2 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai2 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai2 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai5 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai5 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara