Labarai
Ku Kyale Kananan Hukumomi Su Ci Gashin Kansu- Shugaba Tinubu
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya gargadi gwamnonin jihohi da su guji saba hukuncin Kotun Koli da ya bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu game da kuɗadensu, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da rashin bin hukuncin na iya jawo Gwamnatin Tarayya ta shiga tsakani.
Ya jaddada cewa dole ne a mutunta hukuncin tare da aiwatar da shi gaba ɗaya domin ƙarfafa shugabanci a matakin ƙananan hukumomi.
Shugaban ya bayar da wannan gargaɗi ne a yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) karo na 15 na jam’iyyar APC, wanda aka gudanar a Cibiyar Taro ta Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Tinubu ya nuna damuwa kan yadda wasu gwamnatocin jihohi ke ci gaba da riƙe kuɗaɗen rabon da doka ta tanada da ya kamata a bai wa ƙananan hukumomi.
Ya bayyana cewa duk da ya zaɓi nuna haƙuri da girmamawa wajen mu’amala da gwamnonin, Gwamnatin Tarayya na da ikon tilasta bin doka.
Ya yi gargaɗin cewa idan gwamnonin suka ƙi bin hukuncin, Gwamnatin Tarayya na iya fara biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga Asusun Tarayya (Federation Account), bisa tanadin kundin tsarin mulki da kuma umarnin Kotun Koli.
-
Labarai7 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai7 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
-
Labarai7 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai5 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai5 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai5 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai5 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai2 days ago‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa
