Labarai
Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
Daga Abdullahi Shettima
Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya karɓi Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda suka tattauna kan manyan muhimman abubuwan ci gaban jihar musamman a fannoni na noma, ababen more rayuwa da tsaro.
A yayin ganawar, Gwamna Uba Sani ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Ƙasa bisa goyon bayan da gwamnatin tarayya ke bai wa Jihar Kaduna, musamman wajen ci gaban harkokin noma da sarrafa amfanin gona. Ya ce kafa Special Agro-Industrial Processing Zone (SAPZ) da African Quality Assurance Centre (AQAC) ya ɗaga martabar jihar a matsayin jagora wajen ci gaban sarkar samar da kayayyakin noma da kuma faɗaɗa damar fitar da su ƙasashen waje. Shugaban Ƙasa ya yaba da wannan cigaba tare da tabbatar da cikakken goyon bayan gwamnatin tarayya.
Haka kuma, Gwamnan ya bayyana wa Shugaban Ƙasa ci gaba da aikin sabunta harkar sufuri a Kaduna, ciki har da aikin Light Rail da kuma tsarin Bus Rapid Transit (BRT) — wanda shi ne na biyu a Najeriya bayan na Legas. Shugaba Tinubu ya tabbatar da ci gaba da tallafi daga gwamnatin tarayya, tare da yabawa da irin hangen nesan Kaduna a bangaren gine-gine.
Shugaban Ƙasar ya kuma tabbatar da aniyar gwamnati wajen ƙarfafa zaman lafiya da tsaro a fadin Jihar Kaduna, tare da alkawarin gaggauta aikin gyara titin Abuja–Kaduna–Zaria–Kano. Ya jaddada cewa gwamnatin tarayya na aiki kafada da kafada da ajandar cigaban Jihar Kaduna domin samar da raya kasa mai fa’ida ga al’umma da inganta rayuwar ’yan ƙasa.
Karshe.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
