Connect with us

Labarai

Shirin Soil Values Da NAIDA Sun Fito Da Tsarin Saukaka Samun Kayayyakin Gona Ga Manoma

Published

on

Shirin Inganta Noma da Kula da Sauyin Yanayi na Soil Values, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Dillalan Kayayyakin Aikin Gona ta Kasa (NAIDA) ta Arewa maso Yamma, ya ƙaddamar da sabon tsari domin sauƙaƙa samun kayayyakin gona ga ƙananan manoma a yankunan Arewacin Najeriya, da ake kira “one-stop shop a turance.

Jami’ar shirin ta kasa Misis Medina Ayuba Fagbemi, ta bayyana cewa za a samar da shagunan tafi-da-gidanka guda tara da za su kai kayayyaki zuwa sama da al’ummomi 20 a jihohin Kano, Jigawa da Bauchi, inda ake sa ran shirin zai amfanar da kusan ƙananan manoma 7,000.

Ta ce tsarin zai taimaka wajen kusantar da ingantattun iri, taki da magungunan kashe kwari ga manoma, tare da samar da shawarwari na gona, gwajin ƙasa da kuma tantance bayanan manoma ta yanar gizo.

Misis Medinat Fagbemi ta yaba wa manoma da malaman gona da suka amince da wannan tsari, tana ƙarfafa su da su yi aiki da gaskiya da tare da jajircewa.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban kungiyar NAIDA Arewa maso Yamma, Injiniya Abdullahi Muhammad, ya shawarci wadanda suka ci gajiyar shirin da su aiwatar da horon da suka samu yadda ya kamata, yayin da Daraktan Hukumar Sauya Fasalin Noma ta Jigawa, Dr. Saifullahi Umar, ya tabbatar da goyon bayan gwamnatin jihar domin cimma nasarar shirin.

Shirin Soil Values, wanda gwamnatin kasar Netherlands ke tallafawa da Yuro Miliyan 100 na tsawon shekaru goma, an kirkiro sa ne da nufin farfaɗo da ƙasar noma, rage gibin amfanin gona, da farfado da ƙasar da ta lalace a Najeriya da wasu ƙasashen Yammacin Afirka.

 

Usman Muhammad Zaria 

Labarai

Labarai13 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara