Connect with us

Kasuwanci

Jihar Jigawa Ta Halarci Babban Taro Kan Kasuwancin Halal A Malaysia

Published

on

Tawagar gwamnatin jihar Jigawa ta shiga sahun sauran kasashe da suka halarci taron kasa da kasa na Halal da ke gudana a Malaysia (MIHAS), domin neman jari da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa na tattalin arziki.

Tawagar karkashin jagorancin Kwamishinan Harkokin Kiwo, Farfesa Abdurrahman Salim Lawal, ta hada da Dr. Saifullahi Umar, Darakta-Janar na Hukumar Zamanantar da Harkar Noma ta Jihar Jigawa, da kuma Hajiya Aisha Sheik Mujaddadi, Darakta-Janar ta Hukumar Inganta Zuba Jari ta Jihar.

Tuni dai tawagar ta halarci taruka daban-daban yayin isar su kasar ta Malaysia, ciki har da taron Halal Certification Convention, taron kasuwancin Halal na duniya, da  MIHAS Power Talk kan zuba jari ta hanyar Halal, da kuma zaman tattaunawa kan kasuwar Halal da bada shaida.

Farfesa Lawal ya ce Jihar Jigawa na son ta zama cibiyar samar da kayayyakin Halal a yammacin Afirka, ta hanyar nuna ƙarfin ta a bangaren noma, musamman kiwo da kuma amfanin gona.

Ya kara da cewa manufar ita ce samar da haɗin gwiwa da kamfanonin Malaysia, hukumomin gwamnati, da shugabannin masana’antun da ke samar da kayayyakin Halal a fannonin sarrafa nama da noman da aka tabbatar da Halal.

Shigar mu cikin MIHAS wani bangare ne na jajircewar wannan gwamnati wajen bambance hanyoyin samun kudaden shiga da kuma samar da ayyukan yi. Mun yi imani cewa haɗin gwiwa da bayanan da muka samu daga wannan taro za su taimaka wajen jawo jari da kuma samar da damar arziki ga al’ummarmu.” In ji shi.

Tawagar ta kuma gudanar da tarurruka da dama tare da manyan masu ruwa da tsaki na Malaysia domin tattauna batutuwan zuba jari, musayar fasaha, da kuma shirye-shiryen ƙarfafa ƙwarewa.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara