Labarai
Kotu Ta Bayyana Shuruddan Bada Belin Murja Kunya
Babbar kotun jihar Kano ta amince da bada belin shahararriyar yar Tiktok din nan mai suna Murja Ibrahim Kunya.
A hukuncin da ya yanke a ranar Litinin, Mai shari’a Nasiru Saminu ya amince da bada belin Murja Kunya a kan kudi Nera Milyan Dari Biyar tare da kawo mutane biyu da za su tsaya mata .
Daya daga cikin wanda zai tsaya mata, dole ya zama makusancin Murja Kunya na biyu kuma wajibi ne ya kasance yana da kadara a cikin ikon kotun.
Bayan haka, kotun ta umurci hukumar kula da asibitocin jihar Kano da kuma asibitin masu tabin hankali da su tabbatar da sallamar Murja bayan sun cika sharuddan belin.
Kotun ta dage zamanta zuwa ranar 16 ga watan Mayu, 2024 domin sauraren karar.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
