Labarai
Cikar Jigawa Shekaru 34: Gwamna Namadi Ya Yabawa Tsoffin Shugabanni
Gwamna Malam Umar Namadi ya yaba wa shugabannin da suka gabata bisa jajircewa da sadaukarwar da suka yi wajen shimfiɗa tubalin ci gaban jihar tun daga shekarar 1991 zuwa yau.
A taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin Dutse, gwamnan ya ce bikin cika shekaru 34 da kafuwar jihar dama ce ta tunawa, tare da murna da kuma sabunta aniyar ci gaban Jigawa.
Ya bayyana cewa jihar ta samu sauyi a fannoni da dama ciki har da noma, ilimi, kiwon lafiya, hanyoyi da ci gaban zamantakewa. A cewarsa, gwamnatinsa za ta ci gaba da kokari kan waɗannan nasarori tare da bullo da sabbin hanyoyi na bunƙasa jihar.
Namadi ya jaddada kudurinsa na aiwatar da manufofin gwamnatinsa 12, wadanda suka haɗa da samar da ayyukan yi, haɓaka noma, inganta kiwon lafiya da ilimi, da kuma raya ababen more rayuwa.
Ya ce gwamnati ta kaddamar da manyan shirye-shirye a fannoni da dama ciki har da injinan noma, ilimi, kiwon lafiya, hanyoyi da kuma tallafa wa matasa, domin inganta hidima da tabbatar da kyakkyawan shugabanci.
Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su haɗa hannu wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban jihar, yana mai cewa “Ci gaban Jigawa alhaki ne na kowa.”
Ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da inganta tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da jinƙai, domin rage talauci da inganta rayuwar jama’a.
A ƙarshe, Gwamna Namadi ya gode wa jama’ar Jigawa bisa goyon bayan da suke ba shi, yana mai alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta kasance mai gaskiya da rikon amana akoda yaushe.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
