Labarai
Gwamna Namadi Ya Rantsar da Sabbin Kwamishinonin Hukumar Ma’aikata
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya rantsar da sabbin kwamishinonin dindindin guda biyu na Hukumar Ma’aikatan Jihar.
Wadanda aka nada su ne Alhaji Babandi Saleh a matsayin Kwamishina na Dindindin na 2 da kuma Alhaji Ibrahim Adamu Fagam a matsayin Kwamishina na Dindindin na 3. An gudanar da bikin rantsuwar ne a zauren majalisar zartaswa na gidan gwamnati da ke Dutse.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ƙarfafa ma’aikata domin tabbatar da ingantaccen tsarin gudanarwa.

Ya bayyana ma’aikata a matsayin ginshiƙi na aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati, yana mai cewa nadin kwamishinonin dindindin a karon farko wani bangare ne na sabbin sauye-sauyen da ake yi.
Gwamnan ya taya sabbin kwamishinonin murna tare da jan hankalinsu da su yi aiki da gaskiya, ƙwarewa da jajircewa.
Ya nuna kwarin gwiwa cewa sabbin kwamishinonin za su bayar da gudummawa sosai ga cigaban Jihar Jigawa.

Da yake jawabi a madadin wadanda aka nada, Alhaji Babandi Saleh ya gode wa gwamnan bisa amincewa da su, tare da yin alkawarin jajircewa wajen aiwatar da shirin sauye-sauyen gwamnati.
Ya tabbatar da cewa za a samu haɗin kai tsakanin Hukumar Ma’aikata da sauran hukumomi domin kawo canji mai kyau.
Alhaji Saleh ya kuma yi alkawarin cewa kwamishinonin ba za su ci amanar gwamnati da al’umma ba, za su kuma yi aiki tukuru don tabbatar da burin da ake da shi a kansu.
Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki a harkar ma’aikatan jihar.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
