Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Gina Titi Mai Nisan Kilomita 35 A Karamar Hukumar Jahun

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada kudurinta na rage wa manoma wahalhalu wajen jigilar amfanin gonakinsu zuwa kasuwanni mafi kusa a fadin jihar.

Gwamna Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da aikin gina titi kimanin kilomita 35 daga Kwanar Idonduna, Kadowawa, Gangawa zuwa Kwanar Olayinka a karamar hukumar Jahun.

A cewarsa, an bai wa wani kamfani aikin a kan kudi Naira Biliyan 12 da miliyan 900 tare da wa’adin watanni 24.

Gwamnan ya kara da cewa samar da hanyoyin shiga da fita na nufin inganta sufuri na jama’a da kayayyaki da kuma rage radadin da manoma ke fuskanta.

Ya bayyana cewa wannan gwamnati ta kammala tituna 25 daga cikin 26 da ta gada daga gwamnatin da ta gabata.

Namadi ya kara da cewa titin Kwanar Idonduna yana daga cikin tituna 47 da wannan gwamnati ta bayar da kwangilar gina su a kan kudi sama da Naira Biliyan 300.

Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan Ayyuka da Sufuri na jihar, Injiniya Gambo S. Malam, ya ce gwamnatin jihar tana ci gaba da gina titunan cikin gari a Aujara a kan kudi Naira Biliyan 3 da miliyan 400.

Ya kara da bayyana cewa, gwamnatin jihar tana kuma aikin gina hanyoyin kauyuka a matsayin wani bangare na kokarin inganta matsayin tattalin arzikin al’ummomin karkara.

 

Usman Muhammad Zaria

 

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara