Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Raba Kayayyakin Lafiyar Mata Da Yara Kyauta

Published

on

Hukumar Kula da Lafiya A Matakin Farko ta Jihar Kano (KSPHCMB) ta fara raba kayayyakin kula da mata masu juna biyu, da kananan yara kyauta a cibiyoyin kula da lafiya na matakin farko guda 106 a fadin jihar.

Wannan shiri na daga cikin alkawuran Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta damar samun lafiya ga mata da yara.

 

A yayin bikin kaddamar da rabon, Darakta Janar na KSPHCMB, Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ya bayyana cewa kayayyakin za su taimaka wajen rage mace-mace da ake iya kaucewa na mata masu juna biyu da yara, ta hanyar karfafa tsarin lafiyar matakin farko a Kano.

 

Ya umurci Daraktocin Yankuna da Shugabannin Sassa (HODs) da su tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen rabon kayayyakin.

Darakta Janar din ya gargadi duk wata karkatarwa ko almundahanar kayayyakin, inda ya jaddada cewa hukumar za ta sa ido sosai don tabbatar da cewa kayan sun isa ga wadanda suka dace.

Farfesa Salisu ya jinjinawa Gwamna Abba bisa cika alkawuran zabe da kuma fifita lafiyar mata da yara, tare da godewa Kwamishinan Lafiya, Dr. Labaran Abubakar Yusuf, bisa goyon baya da kyakkyawan jagoranci wajen ci gaban harkar lafiya a jihar.

Shi ma Daraktan Sashen Magunguna, Pharmacist Abdullahi Abubakar Danzabuwa, ya tabbatar da cewa kayayyakin suna da inganci sosai, kuma za a raba su bisa ka’idojin kasa da kasa na tsarin rabon magunguna da kayayyakin lafiya.

Hukumar  ta KSPHCMB ta bayyana tabbacin cewa shirin zai inganta lafiyar mata da yara a jihar Kano, tare da kara tabbatar da jihar Kano a matsayin jagora a harkar lafiya a matakin farko a Najeriya.

 

Daga Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara