Connect with us

Fasaha

Najeriya Ta Karɓo Rancen Dala Biliyan 1.3 Don Kammala Layin Dogon Kano Zuwa Maraɗi

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.3 domin kammala aikin titin jirgin ƙasa daga Kano zuwa Maraɗi da ke Jamhuriyyar Nijar.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin sanarwar da Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya ta yi a ranar Laraba.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa kamfanin gine-gine na ƙasar China, CCECC, ne zai samar da kaso 85 na kuɗaɗen da ake buƙata.

Haka kuma, ma’aikatar ta ce Gwamnatin Najeriya da haɗin gwiwar Bankin habaka tattalin arzikin Afirka na Africa Development Bank ne ke ɗaukar nauyin aikin.

“Samun bashin na dala biliyan 1.3 na nuna irin nasarar da za a samu wajen kammala layin dogon,” in ji sanarwar.

Wannan dai na ɗaya daga cikin shirye-shiryen Gwamnatin Najeriya na inganta harkar sufuri a faɗin ƙasar domin bunkasa tattalin arziki da ke fama da masassara.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai10 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai4 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai4 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai4 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi4 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai5 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai5 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai6 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai6 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai6 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara