Labarai
Gidauniyar Dangote Ta Kai Tallafin Abinci Ga Wadanda Iftila’in Gobara Ya Shafa A Jigawa
Mazauna Ƙauyen Batakashi da ke ƙaramar hukumar Garki a Jihar Jigawa sun yaba wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa tallafin abinci da ta kai musu.
Wasu daga cikin mazaunan da suka tattauna da wakilinmu sun bayyana farin cikinsu kan wannan karamci, tare da fatan alheri ga gidauniyar.
Daya daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin, Malam Umar Abdullahi, ya ce gidauniyar ta kawo sassauci ga al’umma bayan iftila’in gobara da ya cinye gidaje kusan 45 a kwanan nan.

Haka shi ma Malam Usman Auwal, ya nuna farin cikinsa, inda ya yaba da gwamnatin jihar Jigawa da kuma Gidauniyar Dangote, bisa tallafinsu ga al’umma.
A jawabinsa yayin kaddamar da rabon tallafin na buhunan shinkafa guda 500 masu nauyin kilogiram10, Shugaban ƙaramar hukumar Garki, Alhaji Adamu Kore, ya gode wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa ƙoƙarinta wajen taimakawa al’umma masu rauni a wannan lokaci da suke cikin bukatar.
Ya bayyana cewa wannan tallafi zai rage wa jama’ar ƙauyen Batakashi raɗaɗin halin da suka shiga sakamakon gobarar.
“Muna matuƙar farin ciki da tallafin Dangote da na gwamnatin jihar Jigawa, domin wannan gudummawa ta faranta ran daruruwan iyalai ba kawai a Jigawa ba har da sauran sassan ƙasar nan gaba ɗaya,” in ji Kore.
A nasa jawabin, Mukaddashin Shugaban Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), Alhaji Muhammad Murtala, ya ce Gidauniyar Dangote ta kawo buhunan shinkafa 40,000 masu nauyin kilo 10, domin rabawa talakawa da mabukata.

Maiunguwa, wanda kuma shi ne Daraktan Harkokin Gudanarwa da Kuɗi na hukumar, ya ce a ƙarƙashin gwamnatin Namadi, hukumar ta raba tallafi ga al’ummomi da iftila’i ko matsanancin talauci ya shafa.
Wakilin Gidauniyar Aliko Dangote, Alhaji Mustapha Umar, ya ce gidauniyar tana ba da tallafi ga al’ummomi a faɗin Najeriya domin rage wa marasa ƙarfi raɗaɗi.
Ya ce, “Dangote na shirye koyaushe ya taimaka wa ‘yan Najeriya ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote, wadda aka ƙirƙira domin aiwatar da ayyukan jinƙai.”
Radio Nigeria ya ruwaito cewa Gidauniyar ta bayar da buhunan shinkafa 500 masu kilo 10 da tabarma 100 ga al’ummar Batakashi da ke yankin Garki a jihar Jigawa, waɗanda gobara ta shafa.
Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa ce ta jagoranci aikin rabon kayan tallafin.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
