Connect with us

Labarai

Gidauniyar Dangote Ta Kai Tallafin Abinci Ga Wadanda Iftila’in Gobara Ya Shafa A Jigawa

Published

on

Mazauna Ƙauyen Batakashi da ke ƙaramar hukumar Garki a Jihar Jigawa sun yaba wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa tallafin abinci da ta kai musu.

Wasu daga cikin mazaunan da suka tattauna da wakilinmu sun bayyana farin cikinsu kan wannan karamci, tare da fatan alheri ga gidauniyar.

Daya daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin, Malam Umar Abdullahi, ya ce gidauniyar ta kawo sassauci ga al’umma bayan iftila’in gobara da ya cinye gidaje kusan 45 a kwanan nan.

Haka shi ma Malam Usman Auwal,  ya nuna farin cikinsa, inda ya yaba da gwamnatin jihar Jigawa da kuma Gidauniyar Dangote, bisa tallafinsu ga al’umma.

A jawabinsa yayin kaddamar da rabon tallafin na buhunan shinkafa guda 500 masu nauyin kilogiram10, Shugaban ƙaramar hukumar Garki, Alhaji Adamu Kore, ya gode wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa ƙoƙarinta wajen taimakawa al’umma masu rauni a wannan lokaci da suke cikin bukatar.

Ya bayyana cewa wannan tallafi zai rage wa jama’ar ƙauyen Batakashi raɗaɗin halin da suka shiga sakamakon gobarar.

Muna matuƙar farin ciki da tallafin Dangote da na gwamnatin jihar Jigawa, domin wannan gudummawa ta faranta ran daruruwan iyalai ba kawai a Jigawa ba har da sauran sassan ƙasar nan gaba ɗaya,” in ji Kore.

A nasa jawabin, Mukaddashin Shugaban Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), Alhaji Muhammad Murtala, ya ce Gidauniyar Dangote ta kawo buhunan shinkafa 40,000 masu nauyin kilo 10, domin rabawa talakawa da mabukata.

Maiunguwa, wanda kuma shi ne Daraktan Harkokin Gudanarwa da Kuɗi na hukumar, ya ce a ƙarƙashin gwamnatin Namadi, hukumar ta raba tallafi ga al’ummomi da iftila’i ko matsanancin talauci ya shafa.

Wakilin Gidauniyar Aliko Dangote, Alhaji Mustapha Umar, ya ce gidauniyar tana ba da tallafi ga al’ummomi a faɗin Najeriya domin rage wa marasa ƙarfi raɗaɗi.

Ya ce, “Dangote na shirye koyaushe ya taimaka wa ‘yan Najeriya ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote, wadda aka ƙirƙira domin aiwatar da ayyukan jinƙai.”

Radio Nigeria ya ruwaito cewa Gidauniyar ta bayar da buhunan shinkafa 500 masu kilo 10 da tabarma 100 ga al’ummar Batakashi da ke yankin Garki a jihar Jigawa, waɗanda gobara ta shafa.

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa ce ta jagoranci aikin rabon kayan tallafin.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara