Labarai
Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
Shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Muhammad Uba Builder, ya sake jaddada kudirinsa na kyakkyawan shugabanci wajen gudanar da harkokin karamar hukumar.
Ya bada wannan tabbaci ne yayin rabon Naira dubu hamsin hamsin ga mutane 70 da suka amfana da shirin noman alkama da karamar hukumar ta kirkiro.
A cewarsa, mutane 165 ne aka saka cikin shirin, inda matasa 70 daga ciki ‘yan siyasa ne, wadanda a ke da bukatar canza rayuwarsu zuwa hanyoyin neman na kai, duba da cewa siyasa ba sana’a ba ce, illa tsarin shugabanci ne.
Alhaji Muhammad Uba Builder ya ce an samar wa mahalarta shirin da filin noma, tare da gyaran filin, da samar da irin alkama da sauran abubuwan bukata, yayin da suke lura da gonakin har zuwa lokacin girbi.
Ya ce kasancewar wadannan ‘yan siyasa sabbin shiga harkar noma ne yasa ba su samu gagarumar nasara ba, don haka akwai bukatar a kara tallafa musu da jari domin su shiga kananan sana’o’i, yayin da karamar hukumar za ta hada kai da hukumar manoma da makiyaya domin samar musu da kadada daya ta noma ga kowanensu domin su yi noma na damina.
Shugaban ya bukaci jama’a da su yi watsi da jita-jita, su kasance masu juriya, da addu’a ga shugabanni domin su gudanar da aikinsu bisa adalci da gaskiya.
Da suke magana a madadin ‘yan siyasa, Usman Sarki da Bello Ajayi sun sake jaddada kudurinsu na kare mutuncin jihar da shugaban karamar hukumar tare da alkawarin shiga harkokin da za su inganta rayuwarsu ta tattalin arziki.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai19 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
