Connect with us

Ilimi

UNICEF Ya Kara Jan Hankalin Gwamnatin Najeriya Game Da Ilimin ‘Ya’ya Mata

Published

on

Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su kara himma wajen yara mata na samun damar yin karatu.

Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Farah, ne ya yi wannan kiran a Kano a wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta 2025.

Ya kara da cewa alkaluma sun nuna cewa ‘yan mata miliyan 7 da 600 ba sa zuwa makaranta, inda shiyyar Arewa maso Yamma da arewa maso gabas ke da kashi 48 cikin 100 na adadin.

Ya danganta wannan kididdigar da abubuwan da suka hada da talauci da ka’idojin zamantakewa da nuna wariyar jinsi, wadanda ke dakile bai wa ‘ya’ya mata damar samun ilimi.

A lokacin da yake gabatar da bitar ayyukan UNICEF na inganta karatun yara mata da kuma ci gaba da karatu, shugaban ofishin kula da kananan yara na jihar Kano, Rahama Mohammed Farah, ya ce asusun ya samu  hadin gwiwa da gwamnati da al’umma wajen magance matsalolin.

Ya ce UNICEF ta kuma yi amfani da tallafin kudi da sauran abubuwan karfafa gwiwa don karfafawa iyaye gwiwa, su yi rajistar ‘ya’yansu mata da tabbatar da ganin sun ci gaba da zuwa makaranta.

Ya yi bayanin cewa, “UNICEF ya yi kokari matuka a wannan fanni, ciki har da bayar da kudade domin karfafa musu gwiwa wajen tura ‘ya’yansu mata zuwa makaranta tare da tallafa musu zuwa matakin sakandare”.

Ya yi bayanin yadda asusun ya ke inganta fasahar rubutu da karatun ‘ya’ya mata ta hanyar cibiyoyin karatun ‘yan mata don ‘yan mata (G4G), inda kimanin ‘yan mata da ke zuwa makaranta miliyan 2 da 600 su ke samun ilimi ta hanyoyin sadarwa da suka hada da rediyo da talabijin a hakin yanzu.

UNICEF ya kuma inganta kwazon malamai don ilmantar da ‘ya’ya mata, tare da kara yawan malamai a makarantun firamare 42,000“, inji Farah.

Ya yi bayanin cewa UNICEF ya kuma gina tare da gyara wuraren tsaftar ruwa a makarantu 33 a fadin jihohin Kano da Jigawa,  wadanda ‘yan mata 19,622 ke amfani da su.

Ya ce asusun yana kuma  aiki tare da masu tsara manufofi a fannin ilimi don tabbatar da ingantacciyar kariya ga yara da ayyukan makaranta ga yara mata, yayin da kuma yana inganta kwazon malamai  da za su  jagoranci  yara mata.

Taron manema labaran ya samu halartar ‘yan jaridu  daga jihohin Kano,  da Jigawa da Katsina.

Usman Mohammed da Isma’il Adamu

Labarai

Labarai18 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara