Labarai
An wanke mata uku daga zargin safarar miyagun Kwayoyi a Saudiyya
Hukumomi a ƙasar Saudiyya sun wanke wasu ƴan Najeriya mata guda uku da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi.
Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ce ta fitar da sanarwar hakan, a jiya Lahadi, inda ta ce an kama su ne a ranar 5a ga watan Maris na shekarar 2024 a birnin Madina.
Sanarwar ta ce matan su ne: Hadiza Abba da Fatima Umater Malah da Fatima Kannai Gamboi, kuma an sake su ne bayan wata goma ana shari’a a ƙasar.
An kama matan ne bayan an kama wasu mutum biyu ƴan Najeriya da miyagun ƙwayoyi da suka haɗa da hodar ibilis, inda aka zargi matan da taimakonsu wajen shigar da ƙwayoyin zuwa ƙasar.
Sanarwar ta ƙara da cewa an miƙa matan ga ofishin jakadancin Najeriya da ke Saudiyya, kuma tuni aka fara shirye-shiryen mayar da su ƙasarsu Najeriya.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
