Ilimi
Al’ummar Musulmi Sun Yi Addu’a Ta Musamman Ga Gwamna Kefas
Al’ummar musulmin jihar Taraba sun gudanar da karatun kur’ani mai tsarki tare da gudanar da addu’o’i na musamman ga gwamna Agbu Kefas da al’ummar jihar Taraba.
An gudanar da addu’ar ce a masallacin Juma’a na Saurara da ke Jalingo, babban birnin jihar a ranar Asabar 4 ga watan Janairu, 2025.
An fara shirin ne da karatun kur’ani mai tsarki, sannan aka gudanar da addu’o’i na musamman karkashin jagorancin manyan limamai na wasu masallatan Juma’a na jihar.
A karkashin jagorancin Malam Hussaini Isma’ila, mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin addinin musulmi, taron ya hada manyan limamai da malaman addinin musulunci daga kananan hukumomin jihar 16.
Malaman addinin Islama sun nuna godiyarsu ga Gwamna Agbu Kefas bisa namijin kokarin da yake yi na gina babbar jihar Taraba ga kowa da kowa.
A cikin addu’o’in da suka yi, malamai sun roki Allah ya ci gaba da yi masa jagora, ya ba shi lafiya, da nasara mai dorewa ga Gwamna da tawagarsa.
Malam Hussaini Ismaila, mai baiwa gwamna Agbu Kefas shawara kan harkokin addinin musulmi, ya karkare taron da kira ga ‘yan uwa musulmi na jihar Taraba da su hada kai da goyon bayan gwamnatin Gwamna Kefas.
Taron addu’o’i na musamman da Malam Hussaini Isma’ila ya shirya ya nuna kyakykyawar alaka tsakanin al’ummar Musulmi da gwamnatin Gwamna Agbu Kefas a halin yanzu, da kuma sadaukarwar da suke yi na samar da zaman lafiya da hadin kai da ci gaba.
Sani Sulaiman/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
