Kasuwanci
Gwamna Namadi Yasha Alwashin Bunkasa Jihar Jigawa
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya ce gwamnati ta sanya jihar a cikin wani tushe na farfado da tattalin arziki da wadata cikin shekara daya da ta gabata.
Gwamnan ya bayyana haka ne a jawabin da ya yi wa al’ummar jihar domin cika shekara guda a kan karagar mulki.
Ya ce, shekara daya da ta wuce an rantsar da shi a matsayin Gwamnan Jihar Jigawa, kuma a yau suna bikin cika shekara guda na sadaukar da kai da aka samu da ci gaba.
Malam Umar Namadi ya ci gaba da bayanin cewa, a cikin shekarar da ta gabata, gwamnatin da ke ci yanzu ta taba rayuwar dubban mutane ta hanyar inganta tattalin arzikinsu, ayyukan daukar ma’aikata da tsare-tsaren inshorar lafiya.
Sauran sun hada da kara samar da abinci tare da ayyukan noma da kuma inganta ababen more rayuwa.
Ya ce, wadannan nasarorin na nuni ne da jajircewarsu wajen kyautata rayuwar al’ummar jihar.
“Ina mika godiyata ga ‘yan majalisar zartarwa ta jiha, ‘yan majalisar jiha, ma’aikatan shari’a, masu rike da mukaman siyasa da ma’aikatan gidan gwamnati.”
A cewarsa, yayin da suke yin la’akari da wadannan nasarori, sun yi alkawarin ci gaba da yi wa jiharsu da al’ummarta hidima da sadaukarwa da.
KARSHE/USMAN MZ/Wababe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
